< Ishaya 63 >

1 Wane ne wannan mai zuwa daga Edom, daga Bozra, saye da jajjayen rigunarsa? Wane ne wannan, sanye cikin daraja, tafe cikin girmar ƙarfinsa? “Ni ne, mai magana cikin adalci, mai ikon ceto.”
Qui est celui-ci qui vient d'Edom, de Botsra, ayant les habits teints en rouge; celui-ci qui est magnifiquement paré en son vêtement, marchant selon la grandeur de sa force? C'est moi qui parle en justice, et qui ai tout pouvoir de sauver.
2 Me ya sa rigunanka suka yi ja, sai ka ce na wanda yake tattaka’ya’yan inabi?
Pourquoi y a-t-il du rouge en ton vêtement? et pourquoi tes habits sont-ils comme les habits de ceux qui foulent au pressoir?
3 “Na tattake’ya’yan inabi ni kaɗai; cikin al’ummai kuma babu wani tare da ni. Na tattake su cikin fushina Na matse su cikin hasalata; jininsu ya fantsamar wa rigunana, na kuma ɓata dukan tufafina.
J'ai été tout seul à fouler au pressoir, et personne d'entre les peuples n'a été avec moi; cependant j'ai marché sur eux en ma colère, et je les ai foulés en ma fureur; et leur sang a rejailli sur mes vêtements, et j'ai souillé tous mes habits.
4 Gama ranar ɗaukan fansa tana a cikin zuciyata, kuma shekarar fansata ta zo.
Car le jour de la vengeance est dans mon cœur, et l'année en laquelle je dois racheter les miens, est venue.
5 Na duba, amma babu wanda zai taimaka, na yi mamaki cewa ba wanda ya goyi baya; saboda haka hannuna ya yi mini ceto, fushina kuma ya rayar da ni.
J'ai donc regardé, et il n'y a eu personne qui m'aidât; et j'ai été étonné, et il n'y a eu personne qui me soutînt; mais mon bras m'a sauvé, et ma fureur m'a soutenu.
6 Na tattake al’ummai cikin fushina; cikin hasalata kuma na sa sun bugu na kuma zub da jininsu a ƙasa.”
Ainsi j'ai foulé les peuples en ma colère, et je les ai enivrés en ma fureur; et j'ai abattu leur force par terre.
7 Zan ba da labarin alherin Ubangiji, ayyukan da suka sa a yabe shi, bisa ga dukan abubuwan da Ubangiji ya yi mana, I, ayyuka masu kyan da ya yi domin gidan Isra’ila, bisa ga jinƙansa da yawan alheransa.
Je ferai mention des gratuités de l'Eternel, qui sont les louanges de l'Eternel, à cause de tous les bienfaits que l'Eternel nous a faits; car grand est le bien de la maison d'Israël, lequel il leur a fait selon ses compassions, et selon la grandeur de ses gratuités.
8 Ya ce, “Babu shakka su mutanena ne,’ya’ya maza waɗanda ba za su ruɗe ni ba”; ta haka ya zama Mai Cetonsu.
Car il a dit; quoi qu'il en soit, ils sont mon peuple, des enfants qui ne dégénéreront point; et il leur a été Sauveur.
9 Cikin dukan damuwarsu shi ma ya damu, mala’ikan da yake gabansa ya cece su. Cikin ƙauna da jinƙai ya fanshe su; ya kuma ɗaga su ya riƙe su dukan kwanakin dā
Et dans toute leur angoisse il a été en angoisse, et l'Ange de sa face les a délivrés; lui-même les a rachetés par son amour et sa clémence, et il les a portés, et les a élevés en tout temps.
10 Duk da haka suka yi tawaye suka ɓata wa Ruhu Mai Tsarki rai. Saboda haka ya juya ya kuma zama abokin gābansu shi kansa kuma ya yaƙe su.
Mais ils ont été rebelles, et ils ont contristé l'Esprit de sa sainteté, c'est pourquoi il est devenu leur ennemi, [et] il a lui-même combattu contr'eux.
11 Sa’an nan mutanensa suka tuna kwanakin dā, kwanakin Musa da mutanensa, ina yake shi wanda ya fitar da su ta teku, da makiyayan garkensa? Ina shi yake wanda ya sa Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu,
Et on s'est souvenu des jours anciens de Moïse, [et] de son peuple. Où est celui, [a-t-on dit], qui les faisait remonter hors de la mer, avec les pasteurs de son troupeau? où est celui qui mettait au milieu d'eux l'Esprit de sa sainteté;
12 wanda ya aika hannu ɗaukakarsa mai iko ya kasance a hannun dama na Musa, wanda ya raba ruwaye a gabansu, don yă sami wa kansa madawwamin suna,
Qui les menait étant à la main droite de Moïse, par le bras de sa gloire? qui fendait les eaux devant eux, afin qu'il s'acquît un nom éternel?
13 wanda ya bishe su cikin zurfafa? Kamar doki a fili, ba su yi tuntuɓe ba;
Qui les menait par les abîmes, [et] ils n'y ont point bronché, non plus que le cheval dans un lieu de pâturage?
14 kamar shanun da suke gangarawa zuwa kwari, haka Ruhun Ubangiji ya ba su hutu. Ga yadda ka bishe mutanenka don ka ba wa kanka suna mai ɗaukaka.
L'Esprit de l'Eternel les a menés tout doucement comme on mène une bête qui descend dans une plaine; tu as ainsi conduit ton peuple, afin de t'acquérir un nom glorieux.
15 Ka duba daga sama ka gani daga kursiyinka da yake bisa, mai tsarki da kuma mai ɗaukaka. Ina kishinka da kuma ikonka? Ka janye juyayi da kuma tausayin da kake yi mana daga gare mu.
Regarde des cieux, et vois de la demeure de ta sainteté et de ta gloire. Où est ta jalousie, et ta force, et l'émotion bruyante de tes entrailles et de tes compassions, lesquelles se sont retenues envers moi?
16 Amma kai Ubanmu ne, ko Ibrahim bai san mu ba Isra’ila kuma bai yarda da mu ba; kai, ya Ubangiji, kai ne Ubanmu, Mai Fansarmu tun fil azal ne sunanka.
Certes tu es notre Père, encore qu'Abraham ne nous reconnût point, et qu'Israël ne nous avouât point; Eternel, c'est toi qui es notre Père, et ton Nom est notre Rédempteur de tout temps.
17 Don me, ya Ubangiji, ka sa muna barin hanyoyinka muka kuma taurare zukatanmu don kada mu girmama ka? Ka komo domin darajar bayinka, kabilan da suke abin gādonka.
Pourquoi nous as-tu fait égarer, ô Eternel! hors de tes voies, et pourquoi as-tu aliéné notre cœur de ta crainte? retourne-toi en faveur de tes serviteurs, en faveur des Tribus de ton héritage.
18 Gama a ɗan lokaci mutanenka suka mallaki wurinka mai tsarki, amma yanzu abokan gābanmu sun tattake wurinka mai tsarki.
Le peuple de ta sainteté a été en possession bien peu de temps; nos ennemis ont foulé ton Sanctuaire.
19 Mu naka tun fil azal; ba ka taɓa yin mulki a kansu ba, ba a taɓa kira su da sunanka ba.
Nous avons été [comme ceux] sur lesquels tu ne domines point depuis longtemps, et sur lesquels ton Nom n'est point réclamé.

< Ishaya 63 >