< Ishaya 63 >

1 Wane ne wannan mai zuwa daga Edom, daga Bozra, saye da jajjayen rigunarsa? Wane ne wannan, sanye cikin daraja, tafe cikin girmar ƙarfinsa? “Ni ne, mai magana cikin adalci, mai ikon ceto.”
Who is this that cometh fro Edom, in died clothis fro Bosra? this fair man in his `long cloth, goynge in the multitude of his vertu? Y that speke riytfulnesse, and am a forfiytere for to saue.
2 Me ya sa rigunanka suka yi ja, sai ka ce na wanda yake tattaka’ya’yan inabi?
Whi therfor is thi clothing reed? and thi clothis ben as of men stampynge in a pressour?
3 “Na tattake’ya’yan inabi ni kaɗai; cikin al’ummai kuma babu wani tare da ni. Na tattake su cikin fushina Na matse su cikin hasalata; jininsu ya fantsamar wa rigunana, na kuma ɓata dukan tufafina.
Y aloone stampide the presse, and of folkis no man is with me; Y stampide hem in my stronge veniaunce, and Y defoulide hem in my wraththe; and her blood is spreynt on my clothis, and Y made foul alle my clothis.
4 Gama ranar ɗaukan fansa tana a cikin zuciyata, kuma shekarar fansata ta zo.
For whi a dai of veniaunce is in myn herte, and the yeer of my yeldyng cometh.
5 Na duba, amma babu wanda zai taimaka, na yi mamaki cewa ba wanda ya goyi baya; saboda haka hannuna ya yi mini ceto, fushina kuma ya rayar da ni.
I lokide aboute, and noon helpere was; Y souyte, and noon was that helpide; and myn arm sauyde to me, and myn indignacioun, that helpide me.
6 Na tattake al’ummai cikin fushina; cikin hasalata kuma na sa sun bugu na kuma zub da jininsu a ƙasa.”
And Y defoulide puplis in my stronge veniaunce; and Y made hem drunkun in myn indignacioun, and Y drow doun her vertu in to erthe.
7 Zan ba da labarin alherin Ubangiji, ayyukan da suka sa a yabe shi, bisa ga dukan abubuwan da Ubangiji ya yi mana, I, ayyuka masu kyan da ya yi domin gidan Isra’ila, bisa ga jinƙansa da yawan alheransa.
I schal haue mynde on the merciful doyngis of the Lord, Y schal preche the heriyng of the Lord on alle thingis whiche the Lord yeldide to vs, and on the multitude `of goodis of the hous of Israel, whiche he yaf to hem bi his foryyuenesse, and bi the multitude of hise mercies.
8 Ya ce, “Babu shakka su mutanena ne,’ya’ya maza waɗanda ba za su ruɗe ni ba”; ta haka ya zama Mai Cetonsu.
And the Lord seide, Netheles it is my puple, sones not denyynge, and he was maad a sauyour to hem in al the tribulacioun of hem.
9 Cikin dukan damuwarsu shi ma ya damu, mala’ikan da yake gabansa ya cece su. Cikin ƙauna da jinƙai ya fanshe su; ya kuma ɗaga su ya riƙe su dukan kwanakin dā
It was not set in tribulacioun, and the aungel of his face sauyde hem. In his loue and in his foryyuenesse he ayenbouyte hem, and he bar hem, and reiside hem in alle daies of the world.
10 Duk da haka suka yi tawaye suka ɓata wa Ruhu Mai Tsarki rai. Saboda haka ya juya ya kuma zama abokin gābansu shi kansa kuma ya yaƙe su.
Forsothe thei excitiden hym to wrathfulnesse, and turmentiden the spirit of his hooli; and he was turned in to an enemye to hem, and he ouercam hem in batel.
11 Sa’an nan mutanensa suka tuna kwanakin dā, kwanakin Musa da mutanensa, ina yake shi wanda ya fitar da su ta teku, da makiyayan garkensa? Ina shi yake wanda ya sa Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu,
And he hadde mynde on the daies of the world, of Moises, and of his puple. Where is he, that ledde hem out of the see, with the scheepherdis of his floc? Where is he, that settide the spirit of his holi in the myddil therof;
12 wanda ya aika hannu ɗaukakarsa mai iko ya kasance a hannun dama na Musa, wanda ya raba ruwaye a gabansu, don yă sami wa kansa madawwamin suna,
whiche ledde out Moises to the riyt half in the arm of his maieste? which departide watris bifore hem, that he schulde make to hym silf a name euerlastynge;
13 wanda ya bishe su cikin zurfafa? Kamar doki a fili, ba su yi tuntuɓe ba;
whiche ledde hem out thoruy depthis of watris, as an hors not stumblynge in desert,
14 kamar shanun da suke gangarawa zuwa kwari, haka Ruhun Ubangiji ya ba su hutu. Ga yadda ka bishe mutanenka don ka ba wa kanka suna mai ɗaukaka.
as a beeste goynge doun in the feeld? The Spirit of the Lord was the ledere therof; so thou leddist thi puple, that thou madist to thee a name of glorie.
15 Ka duba daga sama ka gani daga kursiyinka da yake bisa, mai tsarki da kuma mai ɗaukaka. Ina kishinka da kuma ikonka? Ka janye juyayi da kuma tausayin da kake yi mana daga gare mu.
Biholde thou fro heuene, and se fro thin hooli dwellyng place, and fro the seete of thi glorie. Where is thi feruent loue, and thi strengthe, the multitude of thin entrailis, and of thi merciful doyngis?
16 Amma kai Ubanmu ne, ko Ibrahim bai san mu ba Isra’ila kuma bai yarda da mu ba; kai, ya Ubangiji, kai ne Ubanmu, Mai Fansarmu tun fil azal ne sunanka.
Tho withelden hem silf on me. Forsothe thou art oure fadir, and Abraham knew not vs, and Israel knew not vs.
17 Don me, ya Ubangiji, ka sa muna barin hanyoyinka muka kuma taurare zukatanmu don kada mu girmama ka? Ka komo domin darajar bayinka, kabilan da suke abin gādonka.
Thou, Lord, art oure fadir, and oure ayenbiere; thi name is fro the world. Lord, whi hast thou maad vs to erre fro thi weies? thou hast made hard oure herte, that we dredden not thee? be thou conuertid, for thi seruauntis, the lynages of thin eritage.
18 Gama a ɗan lokaci mutanenka suka mallaki wurinka mai tsarki, amma yanzu abokan gābanmu sun tattake wurinka mai tsarki.
Thei hadden as nouyt thin hooli puple in possessioun, and oure enemyes defouliden thin halewyng.
19 Mu naka tun fil azal; ba ka taɓa yin mulki a kansu ba, ba a taɓa kira su da sunanka ba.
We ben maad as in the bigynnyng, whanne thou were not Lord of vs, nethir thi name was clepid to help on vs.

< Ishaya 63 >