< Ishaya 63 >
1 Wane ne wannan mai zuwa daga Edom, daga Bozra, saye da jajjayen rigunarsa? Wane ne wannan, sanye cikin daraja, tafe cikin girmar ƙarfinsa? “Ni ne, mai magana cikin adalci, mai ikon ceto.”
Who is this that cometh from Edom? In scarlet garments from Bozrah? This that is glorious in his apparel, Proud in the greatness of his strength? I that proclaim deliverance, And am mighty to save.
2 Me ya sa rigunanka suka yi ja, sai ka ce na wanda yake tattaka’ya’yan inabi?
Wherefore is thine apparel red, And thy garments like those of one that treadeth the wine-vat?
3 “Na tattake’ya’yan inabi ni kaɗai; cikin al’ummai kuma babu wani tare da ni. Na tattake su cikin fushina Na matse su cikin hasalata; jininsu ya fantsamar wa rigunana, na kuma ɓata dukan tufafina.
I have trodden the wine-vat alone, And of the nations there was none with me. And I trod them in mine anger, And I trampled them in my fury, So that their life-blood was sprinkled upon my garments. And I have stained all my apparel.
4 Gama ranar ɗaukan fansa tana a cikin zuciyata, kuma shekarar fansata ta zo.
For the day of vengeance was in my heart, And the year of my deliverance was come.
5 Na duba, amma babu wanda zai taimaka, na yi mamaki cewa ba wanda ya goyi baya; saboda haka hannuna ya yi mini ceto, fushina kuma ya rayar da ni.
And I looked, and there was none to help, And I wondered, that there was none to uphold; Therefore my own arm wrought salvation for me, And my fury, it sustained me.
6 Na tattake al’ummai cikin fushina; cikin hasalata kuma na sa sun bugu na kuma zub da jininsu a ƙasa.”
I trod down the nations in my anger; I crushed them in my fury, And spilled their blood upon the ground.
7 Zan ba da labarin alherin Ubangiji, ayyukan da suka sa a yabe shi, bisa ga dukan abubuwan da Ubangiji ya yi mana, I, ayyuka masu kyan da ya yi domin gidan Isra’ila, bisa ga jinƙansa da yawan alheransa.
I will celebrate the mercy of Jehovah, the glory of Jehovah, According to all that he hath done for us; His great goodness to the house of Israel, Which he hath bestowed on it in his tender mercy, and his great kindness.
8 Ya ce, “Babu shakka su mutanena ne,’ya’ya maza waɗanda ba za su ruɗe ni ba”; ta haka ya zama Mai Cetonsu.
He said, Truly they are my people; Children that will not be false; So he was their deliverer.
9 Cikin dukan damuwarsu shi ma ya damu, mala’ikan da yake gabansa ya cece su. Cikin ƙauna da jinƙai ya fanshe su; ya kuma ɗaga su ya riƙe su dukan kwanakin dā
In all their straits they had no distress; An angel of his presence saved them; In his love and compassion he redeemed them, He took them up and bore them all the days of old.
10 Duk da haka suka yi tawaye suka ɓata wa Ruhu Mai Tsarki rai. Saboda haka ya juya ya kuma zama abokin gābansu shi kansa kuma ya yaƙe su.
But they rebelled, and grieved his holy spirit; Then did he change himself into their enemy; He himself fought against them.
11 Sa’an nan mutanensa suka tuna kwanakin dā, kwanakin Musa da mutanensa, ina yake shi wanda ya fitar da su ta teku, da makiyayan garkensa? Ina shi yake wanda ya sa Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu,
Then remembered his people the ancient days, the days of Moses, [[saying, ]] Where is he that brought them up from the sea with the shepherd of his flock? Where is he that put his holy spirit within him?
12 wanda ya aika hannu ɗaukakarsa mai iko ya kasance a hannun dama na Musa, wanda ya raba ruwaye a gabansu, don yă sami wa kansa madawwamin suna,
That caused his glorious arm to accompany the right hand of Moses, That divided the water before them, To make to himself an everlasting name?
13 wanda ya bishe su cikin zurfafa? Kamar doki a fili, ba su yi tuntuɓe ba;
That led them through the deep, As a horse through a desert, without stumbling?
14 kamar shanun da suke gangarawa zuwa kwari, haka Ruhun Ubangiji ya ba su hutu. Ga yadda ka bishe mutanenka don ka ba wa kanka suna mai ɗaukaka.
As the herd descendeth into the valley, The spirit of Jehovah led them to rest. So didst thou lead thy people, To make for thyself a glorious name.
15 Ka duba daga sama ka gani daga kursiyinka da yake bisa, mai tsarki da kuma mai ɗaukaka. Ina kishinka da kuma ikonka? Ka janye juyayi da kuma tausayin da kake yi mana daga gare mu.
Look down from heaven, and behold from thy holy and glorious habitation! Where is thy zeal and thy might? Thy pity and compassion for me, are they restrained?
16 Amma kai Ubanmu ne, ko Ibrahim bai san mu ba Isra’ila kuma bai yarda da mu ba; kai, ya Ubangiji, kai ne Ubanmu, Mai Fansarmu tun fil azal ne sunanka.
Thou, surely, art our father; Abraham is ignorant of us, And Israel knoweth us not. Thou, O Jehovah, art our father; Our deliverer wast thou of old.
17 Don me, ya Ubangiji, ka sa muna barin hanyoyinka muka kuma taurare zukatanmu don kada mu girmama ka? Ka komo domin darajar bayinka, kabilan da suke abin gādonka.
Why, O Jehovah, dost thou suffer us to wander from thy ways, And harden our hearts against thy fear? Return, for thy servants' sake, The tribes of thine inheritance!
18 Gama a ɗan lokaci mutanenka suka mallaki wurinka mai tsarki, amma yanzu abokan gābanmu sun tattake wurinka mai tsarki.
But a little while did thy holy people possess the land; Then our enemies trampled upon thy sanctuary.
19 Mu naka tun fil azal; ba ka taɓa yin mulki a kansu ba, ba a taɓa kira su da sunanka ba.
It has been with us as if thou hadst never ruled over us, As if we had not been called by thy name.