< Ishaya 63 >
1 Wane ne wannan mai zuwa daga Edom, daga Bozra, saye da jajjayen rigunarsa? Wane ne wannan, sanye cikin daraja, tafe cikin girmar ƙarfinsa? “Ni ne, mai magana cikin adalci, mai ikon ceto.”
Who is this who comes from Edom, with dyed garments from Bozrah, this who is glorious in his apparel, marching in the greatness of his strength? I who speak in righteousness, mighty to save.
2 Me ya sa rigunanka suka yi ja, sai ka ce na wanda yake tattaka’ya’yan inabi?
Why are thou red in thine apparel, and thy garments like him who treads in the wine vat?
3 “Na tattake’ya’yan inabi ni kaɗai; cikin al’ummai kuma babu wani tare da ni. Na tattake su cikin fushina Na matse su cikin hasalata; jininsu ya fantsamar wa rigunana, na kuma ɓata dukan tufafina.
I have trodden the winepress alone, and of the peoples there was no man with me. Yea, I trod them in my anger, and trampled them in my wrath, and their lifeblood is sprinkled upon my garments, and I have stained all my raiment.
4 Gama ranar ɗaukan fansa tana a cikin zuciyata, kuma shekarar fansata ta zo.
For the day of vengeance was in my heart, and the year of my redeemed has come.
5 Na duba, amma babu wanda zai taimaka, na yi mamaki cewa ba wanda ya goyi baya; saboda haka hannuna ya yi mini ceto, fushina kuma ya rayar da ni.
And I looked, and there was none to help. And I wondered that there was none to uphold. Therefore my own arm brought salvation to me. And my wrath, it upheld me.
6 Na tattake al’ummai cikin fushina; cikin hasalata kuma na sa sun bugu na kuma zub da jininsu a ƙasa.”
And I trod down the peoples in my anger, and made them drunk in my wrath, and I poured out their lifeblood on the earth.
7 Zan ba da labarin alherin Ubangiji, ayyukan da suka sa a yabe shi, bisa ga dukan abubuwan da Ubangiji ya yi mana, I, ayyuka masu kyan da ya yi domin gidan Isra’ila, bisa ga jinƙansa da yawan alheransa.
I will make mention of the loving kindnesses of Jehovah, and the praises of Jehovah, according to all that Jehovah has bestowed on us, and the great goodness toward the house of Israel, which he has bestowed on them according to his mercies, and according to the multitude of his loving kindnesses.
8 Ya ce, “Babu shakka su mutanena ne,’ya’ya maza waɗanda ba za su ruɗe ni ba”; ta haka ya zama Mai Cetonsu.
For he said, Surely, they are my people, sons that will not deal falsely. So he was their Savior.
9 Cikin dukan damuwarsu shi ma ya damu, mala’ikan da yake gabansa ya cece su. Cikin ƙauna da jinƙai ya fanshe su; ya kuma ɗaga su ya riƙe su dukan kwanakin dā
In all their affliction he was afflicted, and the agent of his presence saved them. In his love and in his pity he redeemed them. And he bore them, and carried them all the days of old.
10 Duk da haka suka yi tawaye suka ɓata wa Ruhu Mai Tsarki rai. Saboda haka ya juya ya kuma zama abokin gābansu shi kansa kuma ya yaƙe su.
But they rebelled, and grieved his holy Spirit. Therefore he was turned to be their enemy, and himself fought against them.
11 Sa’an nan mutanensa suka tuna kwanakin dā, kwanakin Musa da mutanensa, ina yake shi wanda ya fitar da su ta teku, da makiyayan garkensa? Ina shi yake wanda ya sa Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu,
Then he remembered the days of old, Moses and his people, saying, Where is he who brought them up out of the sea with the shepherds of his flock? Where is he who put his holy Spirit in the midst of them,
12 wanda ya aika hannu ɗaukakarsa mai iko ya kasance a hannun dama na Musa, wanda ya raba ruwaye a gabansu, don yă sami wa kansa madawwamin suna,
who caused his glorious arm to go at the right hand of Moses, who divided the waters before them, to make himself an everlasting name,
13 wanda ya bishe su cikin zurfafa? Kamar doki a fili, ba su yi tuntuɓe ba;
who led them through the depths, as a horse in the wilderness, so that they stumbled not?
14 kamar shanun da suke gangarawa zuwa kwari, haka Ruhun Ubangiji ya ba su hutu. Ga yadda ka bishe mutanenka don ka ba wa kanka suna mai ɗaukaka.
As the cattle that go down into the valley, the Spirit of Jehovah caused them to rest. So thou led thy people to make thyself a glorious name.
15 Ka duba daga sama ka gani daga kursiyinka da yake bisa, mai tsarki da kuma mai ɗaukaka. Ina kishinka da kuma ikonka? Ka janye juyayi da kuma tausayin da kake yi mana daga gare mu.
Look down from heaven, and behold from the habitation of thy holiness and of thy glory. Where are thy zeal and thy mighty acts? The yearning of thy heart and thy compassions are restrained toward me.
16 Amma kai Ubanmu ne, ko Ibrahim bai san mu ba Isra’ila kuma bai yarda da mu ba; kai, ya Ubangiji, kai ne Ubanmu, Mai Fansarmu tun fil azal ne sunanka.
For thou are our Father, though Abraham knows us not, and Israel does not acknowledge us, thou, O Jehovah, are our Father, our Redeemer, from everlasting is thy name.
17 Don me, ya Ubangiji, ka sa muna barin hanyoyinka muka kuma taurare zukatanmu don kada mu girmama ka? Ka komo domin darajar bayinka, kabilan da suke abin gādonka.
O Jehovah, why do thou make us to err from thy ways, and harden our heart from thy fear? Return for thy servants' sake, the tribes of thine inheritance.
18 Gama a ɗan lokaci mutanenka suka mallaki wurinka mai tsarki, amma yanzu abokan gābanmu sun tattake wurinka mai tsarki.
Thy holy people possessed it but a little while. Our adversaries have trodden down thy sanctuary.
19 Mu naka tun fil azal; ba ka taɓa yin mulki a kansu ba, ba a taɓa kira su da sunanka ba.
We have become as those over whom thou never bore rule, as those who were not called by thy name.