< Ishaya 62 >

1 Saboda Sihiyona ba zan yi shiru ba, saboda Urushalima ba zan huta ba, sai adalcinta ya haskaka kamar hasken safiya, cetonta kuma ya haskaka kamar fitila mai haske.
به‌خاطر صهیون سکوت نخواهم کرد وبه‌خاطر اورشلیم خاموش نخواهم شدتا عدالتش مثل نور طلوع کند و نجاتش مثل چراغی که افروخته باشد.۱
2 Al’ummai za su ga adalcinki, sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki; za a kira ki da sabon suna sunan da bakin Ubangiji zai ambata.
و امت‌ها، عدالت تورا و جمیع پادشاهان، جلال تو را مشاهده خواهند نمود. و تو به اسم جدیدی که دهان خداوند آن را قرار می‌دهد مسمی خواهی شد.۲
3 Za ki zama rawanin daraja a hannun Ubangiji, rawanin sarauta a hannun Allahnki.
و تو تاج جلال، در دست خداوند و افسرملوکانه، در دست خدای خود خواهی بود.۳
4 Ba za a ƙara ce da ke Yasasshiya ba, ko a kira ƙasarki Kango. Amma za a ce da ke Hefziba ƙasarki kuma Bewula; gama Ubangiji zai ji daɗinki, ƙasarki kuma za tă yi aure.
و تودیگر به متروک مسمی نخواهی شد و زمینت رابار دیگر خرابه نخواهند گفت، بلکه تو را حفصیبه و زمینت را بعوله خواهند نامید زیرا خداوند از تومسرور خواهد شد و زمین تو منکوحه خواهدگردید.۴
5 Kamar yadda saurayi kan auri yarinya, haka’ya’yanki maza za su aure ki; kamar kuma yadda ango yakan yi farin ciki da amaryarsa, haka Allahnki zai yi farin ciki da ke.
زیرا چنانکه مردی جوان دوشیزه‌ای رابه نکاح خویش در می‌آورد هم چنان پسرانت تو را منکوحه خود خواهند ساخت و چنانکه داماداز عروس مبتهج می‌گردد هم چنان خدایت از تومسرور خواهد بود.۵
6 Na sa matsara a kan katangarki, ya Urushalima; ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Ku da kuke kira bisa sunan Ubangiji, kada ku ba kanku hutu,
‌ای اورشلیم دیده بانان برحصارهای تو گماشته‌ام که هر روز و هرشب همیشه سکوت نخواهند کرد. ای متذکران خداوند خاموش مباشید!۶
7 kuma kada ku ba shi hutu sai ya kafa Urushalima ya kuma mai da ita yabon duniya.
و او را آرامی ندهیدتا اورشلیم را استوار کرده، آن را در جهان محل تسبیح بسازد.۷
8 Ubangiji ya rantse da hannunsa na dama ta hannunsa kuma mai iko cewa, “Ba zan ƙara ba da hatsinki ya zama abinci ga abokan gābanki ba, baƙi kuma ba za su ƙara shan ruwan inabin wanda kika sha wahala samu ba;
خداوند به‌دست راست خود و به بازوی قوی خویش قسم خورده، گفته است که بار دیگرغله تو را ماکول دشمنانت نسازم و غریبان، شراب تو را که برایش زحمت کشیده‌ای نخواهندنوشید.۸
9 amma waɗanda suka girbe shi za su ci shi su kuma yabi Ubangiji, waɗanda kuma suka tattara’ya’yan inabi za su sha shi a filayen wurina mai tsarki.”
بلکه آنانی که آن را می‌چینند آن راخورده، خداوند را تسبیح خواهند نمود و آنانی که آن را جمع می‌کنند آن را در صحنهای قدس من خواهند نوشید.۹
10 Ku wuce, ku wuce ƙofofi! Ku shirya hanya saboda mutane. Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku kawar da duwatsu. Ku ɗaga tuta saboda al’ummai.
بگذرید از دروازه هابگذرید. طریق قوم را مهیا سازید و شاهراه را بلندکرده، مرتفع سازید و سنگها را برچیده علم را به جهت قوم‌ها برپا نمایید.۱۰
11 Ubangiji ya yi shela ga iyakokin duniya cewa, “Faɗa wa Diyar Sihiyona, ‘Ga Mai Cetonki yana zuwa! Ga ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa yana raka shi.’”
اینک خداوند تااقصای زمین اعلان کرده است، پس به دخترصهیون بگویید اینک نجات تو می‌آید. همانااجرت او همراهش و مکافات او پیش رویش می‌باشد.۱۱
12 Za a ce da shi Tsattsarkar Mutane, Fansassu na Ubangiji; za a kuma ce da ke Wadda Aka Nema Birnin da Ba Za a Ƙara Yashe ta ba.
و ایشان را به قوم مقدس و فدیه شدگان خداوند مسمی خواهند ساخت و تو به مطلوب و شهر غیر متروک نامیده خواهی شد.۱۲

< Ishaya 62 >