< Ishaya 62 >
1 Saboda Sihiyona ba zan yi shiru ba, saboda Urushalima ba zan huta ba, sai adalcinta ya haskaka kamar hasken safiya, cetonta kuma ya haskaka kamar fitila mai haske.
because Zion not be silent and because Jerusalem not to quiet till to come out: come like/as brightness righteousness her and salvation her like/as torch to burn: burn
2 Al’ummai za su ga adalcinki, sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki; za a kira ki da sabon suna sunan da bakin Ubangiji zai ambata.
and to see: see nation righteousness your and all king glory your and to call: call by to/for you name new which lip LORD to pierce him
3 Za ki zama rawanin daraja a hannun Ubangiji, rawanin sarauta a hannun Allahnki.
and to be crown beauty in/on/with hand LORD (and turban *Q(K)*) kingship in/on/with palm God your
4 Ba za a ƙara ce da ke Yasasshiya ba, ko a kira ƙasarki Kango. Amma za a ce da ke Hefziba ƙasarki kuma Bewula; gama Ubangiji zai ji daɗinki, ƙasarki kuma za tă yi aure.
not to say to/for you still Forsaken and to/for land: country/planet your not to say still Desolate for to/for you to call: call by My Delight Is in Her My Delight Is in Her and to/for land: country/planet your Married for to delight in LORD in/on/with you and land: country/planet your rule: to marry
5 Kamar yadda saurayi kan auri yarinya, haka’ya’yanki maza za su aure ki; kamar kuma yadda ango yakan yi farin ciki da amaryarsa, haka Allahnki zai yi farin ciki da ke.
for rule: to marry youth virgin rule: to marry you son: child your and rejoicing son-in-law upon daughter-in-law: bride to rejoice upon you God your
6 Na sa matsara a kan katangarki, ya Urushalima; ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Ku da kuke kira bisa sunan Ubangiji, kada ku ba kanku hutu,
upon wall your Jerusalem to reckon: overseer to keep: guard all [the] day and all [the] night continually not be silent [the] to remember [obj] LORD not quiet to/for you
7 kuma kada ku ba shi hutu sai ya kafa Urushalima ya kuma mai da ita yabon duniya.
and not to give: give quiet to/for him till to establish: establish and till to set: make [obj] Jerusalem praise in/on/with land: country/planet
8 Ubangiji ya rantse da hannunsa na dama ta hannunsa kuma mai iko cewa, “Ba zan ƙara ba da hatsinki ya zama abinci ga abokan gābanki ba, baƙi kuma ba za su ƙara shan ruwan inabin wanda kika sha wahala samu ba;
to swear LORD in/on/with right his and in/on/with arm strength his if: surely yes to give: give [obj] grain your still food to/for enemy your and if: surely no to drink son: type of foreign new wine your which be weary/toil in/on/with him
9 amma waɗanda suka girbe shi za su ci shi su kuma yabi Ubangiji, waɗanda kuma suka tattara’ya’yan inabi za su sha shi a filayen wurina mai tsarki.”
for to gather him to eat him and to boast: praise [obj] LORD and to gather him to drink him in/on/with court holiness my
10 Ku wuce, ku wuce ƙofofi! Ku shirya hanya saboda mutane. Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku kawar da duwatsu. Ku ɗaga tuta saboda al’ummai.
to pass to pass in/on/with gate to turn way: road [the] people to build to build [the] highway to stone from stone to exalt ensign upon [the] people
11 Ubangiji ya yi shela ga iyakokin duniya cewa, “Faɗa wa Diyar Sihiyona, ‘Ga Mai Cetonki yana zuwa! Ga ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa yana raka shi.’”
behold LORD to hear: proclaim to(wards) end [the] land: country/planet to say to/for daughter Zion behold salvation your to come (in): come behold wages his with him and wages his to/for face: before his
12 Za a ce da shi Tsattsarkar Mutane, Fansassu na Ubangiji; za a kuma ce da ke Wadda Aka Nema Birnin da Ba Za a Ƙara Yashe ta ba.
and to call: call by to/for them people [the] holiness to redeem: redeem LORD and to/for you to call: call by to seek city not to leave: forsake