< Ishaya 62 >
1 Saboda Sihiyona ba zan yi shiru ba, saboda Urushalima ba zan huta ba, sai adalcinta ya haskaka kamar hasken safiya, cetonta kuma ya haskaka kamar fitila mai haske.
Because of Zion I will not keep quiet, and because of Jerusalem I will take no rest, till her righteousness goes out like the shining of the sun, and her salvation like a burning light.
2 Al’ummai za su ga adalcinki, sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki; za a kira ki da sabon suna sunan da bakin Ubangiji zai ambata.
And the nations will see your righteousness, and all kings your glory: and you will have a new name, given by the mouth of the Lord.
3 Za ki zama rawanin daraja a hannun Ubangiji, rawanin sarauta a hannun Allahnki.
And you will be a fair crown in the hand of the Lord, and a king's head-dress in the hand of your God.
4 Ba za a ƙara ce da ke Yasasshiya ba, ko a kira ƙasarki Kango. Amma za a ce da ke Hefziba ƙasarki kuma Bewula; gama Ubangiji zai ji daɗinki, ƙasarki kuma za tă yi aure.
You will not now be named, She who is given up; and your land will no longer be named, The waste land: but you will have the name, My pleasure is in her, and your land will be named, Married: for the Lord has pleasure in you, and your land will be married.
5 Kamar yadda saurayi kan auri yarinya, haka’ya’yanki maza za su aure ki; kamar kuma yadda ango yakan yi farin ciki da amaryarsa, haka Allahnki zai yi farin ciki da ke.
For as a young man takes a virgin for his wife, so will your maker be married to you: and as a husband has joy in his bride, so will the Lord your God be glad over you.
6 Na sa matsara a kan katangarki, ya Urushalima; ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Ku da kuke kira bisa sunan Ubangiji, kada ku ba kanku hutu,
I have put watchmen on your walls, O Jerusalem; they will not keep quiet day or night: you who are the Lord's recorders, take no rest,
7 kuma kada ku ba shi hutu sai ya kafa Urushalima ya kuma mai da ita yabon duniya.
And give him no rest, till he puts Jerusalem in her place to be praised in the earth.
8 Ubangiji ya rantse da hannunsa na dama ta hannunsa kuma mai iko cewa, “Ba zan ƙara ba da hatsinki ya zama abinci ga abokan gābanki ba, baƙi kuma ba za su ƙara shan ruwan inabin wanda kika sha wahala samu ba;
The Lord has taken an oath by his right hand, and by the arm of his strength, Truly, I will no longer give your grain to be food for your haters; and men of strange countries will not take the wine for which your work has been done:
9 amma waɗanda suka girbe shi za su ci shi su kuma yabi Ubangiji, waɗanda kuma suka tattara’ya’yan inabi za su sha shi a filayen wurina mai tsarki.”
But those who have got in the grain will have it for their food, and will give praise to the Lord; and those who have got in the grapes will take the wine of them in the open places of my holy house.
10 Ku wuce, ku wuce ƙofofi! Ku shirya hanya saboda mutane. Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku kawar da duwatsu. Ku ɗaga tuta saboda al’ummai.
Go through, go through the doors; make ready the way of the people; let the highway be lifted up; let the stones be taken away; let a flag be lifted up over the peoples.
11 Ubangiji ya yi shela ga iyakokin duniya cewa, “Faɗa wa Diyar Sihiyona, ‘Ga Mai Cetonki yana zuwa! Ga ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa yana raka shi.’”
The Lord has sent out word to the end of the earth, Say to the daughter of Zion, See, your saviour comes; those whom he has made free are with him, and those to whom he has given salvation go before him.
12 Za a ce da shi Tsattsarkar Mutane, Fansassu na Ubangiji; za a kuma ce da ke Wadda Aka Nema Birnin da Ba Za a Ƙara Yashe ta ba.
And they will be named, The holy people, Those whose cause has been taken up by the Lord: and you will be named, Desired, A town not given up.