< Ishaya 62 >
1 Saboda Sihiyona ba zan yi shiru ba, saboda Urushalima ba zan huta ba, sai adalcinta ya haskaka kamar hasken safiya, cetonta kuma ya haskaka kamar fitila mai haske.
Nikech Sayun ok analingʼ, bende nikech Jerusalem ok anasik kalingʼ, nyaka timne makare rieny ka yawruok mar piny, kendo warruokne obed marieny ka mach makakni.
2 Al’ummai za su ga adalcinki, sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki; za a kira ki da sabon suna sunan da bakin Ubangiji zai ambata.
Ogendini none timni makare, kendo ruodhi duto none duongʼ mari; bangʼe noluongi gi nying manyien, ma Jehova Nyasaye biro chaki.
3 Za ki zama rawanin daraja a hannun Ubangiji, rawanin sarauta a hannun Allahnki.
Inibed kondo maber e lwet Jehova Nyasaye bende inibed osimb loch e lwet Nyasachi.
4 Ba za a ƙara ce da ke Yasasshiya ba, ko a kira ƙasarki Kango. Amma za a ce da ke Hefziba ƙasarki kuma Bewula; gama Ubangiji zai ji daɗinki, ƙasarki kuma za tă yi aure.
Ok ginichak giluongi ni Kama Ojwangʼ kata chako pinyi ni kama Odongʼ Gunda. To noluongi ni Hefziba kendo pinyi noluongi ni Beula; nimar Jehova Nyasaye nobed kodi gi mor kendo pinyi nochal gi dhako mokendi.
5 Kamar yadda saurayi kan auri yarinya, haka’ya’yanki maza za su aure ki; kamar kuma yadda ango yakan yi farin ciki da amaryarsa, haka Allahnki zai yi farin ciki da ke.
Kaka wuowi kendo nyako e kaka yawuoti nokendi; to bende kaka ngʼama okendo mor gi chiege, e kaka Nyasachi nobed mamor kodi.
6 Na sa matsara a kan katangarki, ya Urushalima; ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Ku da kuke kira bisa sunan Ubangiji, kada ku ba kanku hutu,
Yaye Jerusalem, aseoro jorit e ohinga mari ok ginilingʼ odiechiengʼ gotieno. Un muluongo nying Jehova Nyasaye kik unyosru,
7 kuma kada ku ba shi hutu sai ya kafa Urushalima ya kuma mai da ita yabon duniya.
kendo kik umiye yweyo nyaka chop olos Jerusalem mi omi obed dala marahuma mipako e piny ngima.
8 Ubangiji ya rantse da hannunsa na dama ta hannunsa kuma mai iko cewa, “Ba zan ƙara ba da hatsinki ya zama abinci ga abokan gābanki ba, baƙi kuma ba za su ƙara shan ruwan inabin wanda kika sha wahala samu ba;
Jehova Nyasaye osesingore gi lwete ma korachwich kendo gi bade maratego ni, “Ok nachak ayie wasiku kaw chambu micham, jopinje mamoko bende ok nochak omadh divai manyien, ma usetiyone matek;
9 amma waɗanda suka girbe shi za su ci shi su kuma yabi Ubangiji, waɗanda kuma suka tattara’ya’yan inabi za su sha shi a filayen wurina mai tsarki.”
to jogo mano kagi ema nochamgi, ka gipako Jehova Nyasaye, bende jogo ma choko olemb mzabibu ema nomadhgi e laru mar kara maler mar lemo.”
10 Ku wuce, ku wuce ƙofofi! Ku shirya hanya saboda mutane. Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku kawar da duwatsu. Ku ɗaga tuta saboda al’ummai.
Kaluru, kaluru dhorangach! Losuru yo ne joga. Buguru, buguru yore! Goluru kite. Tingʼuru bandera malo mondo pinje one.
11 Ubangiji ya yi shela ga iyakokin duniya cewa, “Faɗa wa Diyar Sihiyona, ‘Ga Mai Cetonki yana zuwa! Ga ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa yana raka shi.’”
Jehova Nyasaye oselando wachne e tung pinje duto niya: “Wachne nyar Sayun ni, ‘Ne, Jaresni biro! Ne, michne ni e lwete kendo jogo mosegonyo wuotho kode.’”
12 Za a ce da shi Tsattsarkar Mutane, Fansassu na Ubangiji; za a kuma ce da ke Wadda Aka Nema Birnin da Ba Za a Ƙara Yashe ta ba.
Enoluong-gi ni Oganda Maler, ma Jehova Nyasaye Osewalo; kendo noluongi ni Dala Midwaro Gwedho ma en Dala Maduongʼ Ma Ok Nochak Ojwangʼ.