< Ishaya 61 >

1 Ruhun Ubangiji Mai Iko Duka yana a kaina, domin Ubangiji ya shafe ni domin in yi wa’azi labari mai daɗi ga matalauta. Ya aiko ni in warkar da waɗanda suka karai a zuci, don in yi shelar’yanci don ɗaurarru in kuma kunce’yan kurkuku daga duhu
Herrens, Israels Guds Ånd er over mig, fordi Herren har salvet mig til å forkynne et godt budskap for de saktmodige; han har sendt mig til å forbinde dem som har et sønderbrutt hjerte, til å utrope frihet for de fangne og løslatelse for de bundne,
2 don in yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji da kuma ranar ɗaukan fansar Allahnmu, don in ta’azantar da dukan waɗanda suke makoki,
til å utrope et nådens år fra Herren og en hevnens dag fra vår Gud, til å trøste alle sørgende,
3 in tanada wa waɗanda suke baƙin ciki a Sihiyona, in maido musu rawani mai kyau a maimako na toka, man murna a maimako na makoki, da kuma rigar yabo a maimako na ruhun fid da zuciya. Za a ce da su itatuwan oak na adalci, shukin Ubangiji don bayyana darajarsa.
til å gi de sørgende i Sion hodepryd i stedet for aske, gledes olje i stedet for sorg, lovprisnings klædebon i stedet for en vansmektet ånd, og de skal kalles rettferdighetens terebinter, Herrens plantning til hans ære.
4 Za su sāke gina kufai na dā su raya wurare da aka lalace tun da daɗewa; za su sabunta biranen da aka rurrushe da aka lalace tun zamanai masu yawa da suka wuce.
Og de skal bygge op igjen det som blev ødelagt i eldgammel tid, gjenreise det som har ligget øde fra de første slekter; de skal fornye ødelagte byer, det som har ligget øde fra slekt til slekt.
5 Baƙi za su yi kiwon garkunanki; baƙi za su yi miki noman gonaki da gonakin inabinki.
Og fremmede skal stå og vokte eders hjorder, og utlendinger skal være eders akerdyrkere og vingårdsmenn.
6 Za a kuma kira ku firistocin Ubangiji, za a kira ku masu hidimar Allahnmu. Za ku ci wadatar waɗansu al’ummai, kuma a cikin dukiyarsu za ku yi taƙama.
Men I, I skal kalles Herrens prester, vår Guds tjenere skal de kalle eder; folkenes gods skal I ete, og deres herlighet skal gå over til eder.
7 A maimakon kunyarsu mutanena za su sami rabi riɓi biyu, a maimakon wulaƙanci za su yi farin ciki cikin gādonsu; ta haka za su gāji rabo riɓi biyu a ƙasarsu, da kuma madawwamin farin ciki zai zama nasu.
For eders skam skal I få dobbelt gjengjeld, og de som led vanære, skal nu juble over sin lodd; derfor skal de få dobbelt lodd i sitt land, evig glede skal bli dem til del;
8 “Gama ni, Ubangiji, ina ƙaunar adalci; na ƙi fashi da aikata laifi. Cikin adalcina zan sāka musu in kuma yi madawwamin alkawari da su.
for jeg, Herren, elsker rett og hater urettferdig rov, og trofast vil jeg gi dem deres lønn, og en evig pakt vil jeg gjøre med dem.
9 Za a san da zuriyarsu a cikin al’ummai’ya’yansu kuma a cikin mutane. Dukan waɗanda suka gan su za su san cewa su mutane ne da Ubangiji ya sa wa albarka.”
Og deres ætt skal bli kjent blandt folkene, og deres avkom blandt folkeslagene; alle som ser dem, skal kjenne at de er en ætt Herren har velsignet.
10 Ina jin daɗi ƙwarai a cikin Ubangiji; raina yana farin ciki a cikin Allahna. Gama ya suturce ni da rigunan ceto ya yi mini ado da rigar adalci, yadda ango yakan yi wa kansa ado kamar firist kamar kuma yadda amarya takan sha ado da duwatsunta masu daraja.
Jeg vil glede mig i Herren, min sjel skal fryde sig i min Gud; for han har klædd mig i frelsens klædebon, i rettferdighetens kappe har han svøpt mig, likesom brudgommen, som setter på sig en hue prektig som prestens, og likesom bruden, som pryder sig med sine smykker.
11 Gama kamar yadda ƙasa takan sa tsire-tsire su tohu lambu kuma ya sa iri ya yi girma, haka Ubangiji Mai Iko Duka zai sa adalci da yabo su tsiro a gaban dukan al’ummai.
For som jorden lar sine spirer skyte frem, og som en have lar sine vekster spire, således skal Herren, Israels Gud, la rettferdighet og lovsang fremspire for alle folkenes åsyn.

< Ishaya 61 >