< Ishaya 61 >
1 Ruhun Ubangiji Mai Iko Duka yana a kaina, domin Ubangiji ya shafe ni domin in yi wa’azi labari mai daɗi ga matalauta. Ya aiko ni in warkar da waɗanda suka karai a zuci, don in yi shelar’yanci don ɗaurarru in kuma kunce’yan kurkuku daga duhu
Kuasa TUHAN Yang Mahatinggi ada padaku; Ia memilih dan mengutus aku untuk membawa kabar baik kepada orang miskin dan menyembuhkan orang yang remuk hatinya; untuk mengumumkan kepada orang tahanan bahwa mereka segera dibebaskan, dan kepada orang-orang dalam penjara bahwa mereka akan dilepaskan.
2 don in yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji da kuma ranar ɗaukan fansar Allahnmu, don in ta’azantar da dukan waɗanda suke makoki,
Ia mengutus aku untuk memberitakan bahwa sudah tiba saatnya TUHAN menyelamatkan; untuk menghibur semua yang berduka cita, dan membalas musuh-musuh mereka;
3 in tanada wa waɗanda suke baƙin ciki a Sihiyona, in maido musu rawani mai kyau a maimako na toka, man murna a maimako na makoki, da kuma rigar yabo a maimako na ruhun fid da zuciya. Za a ce da su itatuwan oak na adalci, shukin Ubangiji don bayyana darajarsa.
untuk memberi kegembiraan dan sukacita kepada orang yang bersedih dan berkabung; untuk mengubah kesedihan mereka menjadi lagu pujian. Mereka akan seperti pohon yang ditanam TUHAN sendiri. Mereka akan melakukan yang baik dan benar, sehingga TUHAN diagungkan.
4 Za su sāke gina kufai na dā su raya wurare da aka lalace tun da daɗewa; za su sabunta biranen da aka rurrushe da aka lalace tun zamanai masu yawa da suka wuce.
Mereka akan membangun kota-kota yang sudah lama runtuh dan mendirikan tempat-tempat yang sudah lama sunyi.
5 Baƙi za su yi kiwon garkunanki; baƙi za su yi miki noman gonaki da gonakin inabinki.
Hai, bangsaku, orang asing akan melayani kamu; mereka akan menggembalakan ternakmu dan mengerjakan ladang serta kebun anggurmu.
6 Za a kuma kira ku firistocin Ubangiji, za a kira ku masu hidimar Allahnmu. Za ku ci wadatar waɗansu al’ummai, kuma a cikin dukiyarsu za ku yi taƙama.
Kamu akan disebut hamba Allah dan dinamakan imam TUHAN kita. Kamu akan menikmati kekayaan bangsa-bangsa dan merasa bangga karena harta mereka.
7 A maimakon kunyarsu mutanena za su sami rabi riɓi biyu, a maimakon wulaƙanci za su yi farin ciki cikin gādonsu; ta haka za su gāji rabo riɓi biyu a ƙasarsu, da kuma madawwamin farin ciki zai zama nasu.
Karena kamu sudah mendapat malu dua kali lipat, dan noda serta kehinaan telah menjadi bagianmu, maka kamu mendapat warisan dua kali lipat di negerimu dan memiliki sukacita abadi.
8 “Gama ni, Ubangiji, ina ƙaunar adalci; na ƙi fashi da aikata laifi. Cikin adalcina zan sāka musu in kuma yi madawwamin alkawari da su.
TUHAN berkata, "Aku mencintai keadilan dan membenci penindasan serta kejahatan. Aku akan memberi upahmu dengan setia, dan mengikat janji abadi dengan kamu.
9 Za a san da zuriyarsu a cikin al’ummai’ya’yansu kuma a cikin mutane. Dukan waɗanda suka gan su za su san cewa su mutane ne da Ubangiji ya sa wa albarka.”
Keturunanmu terkenal di mana-mana, termasyhur di antara segala bangsa. Maka semua orang yang melihatnya akan mengakui, bahwa bangsa ini Kuberkati."
10 Ina jin daɗi ƙwarai a cikin Ubangiji; raina yana farin ciki a cikin Allahna. Gama ya suturce ni da rigunan ceto ya yi mini ado da rigar adalci, yadda ango yakan yi wa kansa ado kamar firist kamar kuma yadda amarya takan sha ado da duwatsunta masu daraja.
Yerusalem berkata, "Aku bergembira karena TUHAN, hatiku bersuka ria karena Allah. Seperti pengantin pria dan wanita memakai perhiasan serba indah, begitulah TUHAN mengenakan padaku baju keselamatan dan kemenangan.
11 Gama kamar yadda ƙasa takan sa tsire-tsire su tohu lambu kuma ya sa iri ya yi girma, haka Ubangiji Mai Iko Duka zai sa adalci da yabo su tsiro a gaban dukan al’ummai.
Seperti benih yang ditaburkan akan tumbuh menjadi tanaman, begitulah TUHAN Allah menumbuhkan keselamatan dan semua bangsa akan memuji Dia."