< Ishaya 61 >

1 Ruhun Ubangiji Mai Iko Duka yana a kaina, domin Ubangiji ya shafe ni domin in yi wa’azi labari mai daɗi ga matalauta. Ya aiko ni in warkar da waɗanda suka karai a zuci, don in yi shelar’yanci don ɗaurarru in kuma kunce’yan kurkuku daga duhu
L’esprit du Seigneur est sur moi, parce que le Seigneur m’a oint; pour annoncer sa parole à ceux qui sont doux, il m’a envoyé, pour guérir ceux qui ont le cœur contrit, pour prêcher la grâce aux captifs, et l’ouverture des prisons à ceux qui y sont renfermés;
2 don in yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji da kuma ranar ɗaukan fansar Allahnmu, don in ta’azantar da dukan waɗanda suke makoki,
Pour publier l’année de la réconciliation du Seigneur, et le jour de la vengeance de notre Dieu; pour consoler tous ceux qui pleurent;
3 in tanada wa waɗanda suke baƙin ciki a Sihiyona, in maido musu rawani mai kyau a maimako na toka, man murna a maimako na makoki, da kuma rigar yabo a maimako na ruhun fid da zuciya. Za a ce da su itatuwan oak na adalci, shukin Ubangiji don bayyana darajarsa.
Pour disposer et donner à ceux qui pleurent dans Sion une couronne au lieu de cendre, de l’huile de joie au lieu de deuil, un manteau de louange au lieu d’un esprit de tristesse; et ils seront appelés dans Sion, les héros de la justice, et la plantation du Seigneur pour le glorifier.
4 Za su sāke gina kufai na dā su raya wurare da aka lalace tun da daɗewa; za su sabunta biranen da aka rurrushe da aka lalace tun zamanai masu yawa da suka wuce.
Et ils rempliront d’édifices des lieux déserts depuis des siècles; ils relèveront d’anciennes ruines, et ils rétabliront des cités abandonnées, désolées pendant plusieurs générations.
5 Baƙi za su yi kiwon garkunanki; baƙi za su yi miki noman gonaki da gonakin inabinki.
Et il se trouvera parmi vous des étrangers, et ils feront paître vos troupeaux; et des fils d’étrangers seront vos laboureurs et vos vignerons.
6 Za a kuma kira ku firistocin Ubangiji, za a kira ku masu hidimar Allahnmu. Za ku ci wadatar waɗansu al’ummai, kuma a cikin dukiyarsu za ku yi taƙama.
Mais vous, vous serez appelés les prêtres du Seigneur; on vous nommera les ministres de notre Dieu; vous mangerez la richesse des nations, vous vous enorgueillirez de leur gloire.
7 A maimakon kunyarsu mutanena za su sami rabi riɓi biyu, a maimakon wulaƙanci za su yi farin ciki cikin gādonsu; ta haka za su gāji rabo riɓi biyu a ƙasarsu, da kuma madawwamin farin ciki zai zama nasu.
Au lieu de votre double confusion et honte, ils loueront leur partage; à cause de cela dans leur terre, ils posséderont le double, une joie éternelle sera pour eux.
8 “Gama ni, Ubangiji, ina ƙaunar adalci; na ƙi fashi da aikata laifi. Cikin adalcina zan sāka musu in kuma yi madawwamin alkawari da su.
Parce que moi, le Seigneur, j’aime la justice, et j’ai en haine la rapine dans l’holocauste, j’établirai leur œuvre dans la vérité, je ferai avec eux une alliance perpétuelle.
9 Za a san da zuriyarsu a cikin al’ummai’ya’yansu kuma a cikin mutane. Dukan waɗanda suka gan su za su san cewa su mutane ne da Ubangiji ya sa wa albarka.”
Et on connaîtra sa race parmi les nations, et ses rejetons au milieu des peuples; tous ceux qui les verront reconnaîtront qu’ils sont la race qu’a bénie le Seigneur.
10 Ina jin daɗi ƙwarai a cikin Ubangiji; raina yana farin ciki a cikin Allahna. Gama ya suturce ni da rigunan ceto ya yi mini ado da rigar adalci, yadda ango yakan yi wa kansa ado kamar firist kamar kuma yadda amarya takan sha ado da duwatsunta masu daraja.
Me réjouissant, je me réjouirai dans le Seigneur, mon âme exultera en mon Dieu; parce qu’il m’a revêtu des vêtements du salut, et du manteau de la justice il m’a enveloppé comme l’époux paré d’une couronne, et comme l’épouse ornée de ses colliers.
11 Gama kamar yadda ƙasa takan sa tsire-tsire su tohu lambu kuma ya sa iri ya yi girma, haka Ubangiji Mai Iko Duka zai sa adalci da yabo su tsiro a gaban dukan al’ummai.
Car comme la terre produit son germe, et comme un jardin fait germer sa semence, ainsi le Seigneur Dieu fera germer la justice et la louange devant toutes les nations.

< Ishaya 61 >