< Ishaya 61 >

1 Ruhun Ubangiji Mai Iko Duka yana a kaina, domin Ubangiji ya shafe ni domin in yi wa’azi labari mai daɗi ga matalauta. Ya aiko ni in warkar da waɗanda suka karai a zuci, don in yi shelar’yanci don ɗaurarru in kuma kunce’yan kurkuku daga duhu
L'Esprit du Seigneur l'Eternel est sur moi, c'est pourquoi l'Eternel m'a oint pour évangéliser aux débonnaires, il m'a envoyé pour guérir ceux qui ont le cœur brisé, pour publier aux captifs la liberté, et aux prisonniers l'ouverture de la prison.
2 don in yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji da kuma ranar ɗaukan fansar Allahnmu, don in ta’azantar da dukan waɗanda suke makoki,
Pour publier l'an de la bienveillance de l'Eternel, et le jour de la vengeance de notre Dieu; pour consoler tous ceux qui mènent deuil;
3 in tanada wa waɗanda suke baƙin ciki a Sihiyona, in maido musu rawani mai kyau a maimako na toka, man murna a maimako na makoki, da kuma rigar yabo a maimako na ruhun fid da zuciya. Za a ce da su itatuwan oak na adalci, shukin Ubangiji don bayyana darajarsa.
Pour annoncer à ceux de Sion qui mènent deuil, que la magnificence leur sera donnée au lieu de la cendre; l'huile de joie au lieu du deuil; le manteau de louange au lieu de l'esprit d'accablement; tellement qu'on les appellera les chênes de la justice, et la plante de l'Eternel, pour s'y glorifier.
4 Za su sāke gina kufai na dā su raya wurare da aka lalace tun da daɗewa; za su sabunta biranen da aka rurrushe da aka lalace tun zamanai masu yawa da suka wuce.
Et ils rebâtiront ce qui aura été dès longtemps désert, ils rétabliront les lieux qui auront été auparavant désolés, et ils renouvelleront les villes désertes, et les choses désolées d'âge en âge.
5 Baƙi za su yi kiwon garkunanki; baƙi za su yi miki noman gonaki da gonakin inabinki.
Et les étrangers s'y tiendront, et paîtront vos brebis, et les enfants de l'étranger seront vos laboureurs et vos vignerons.
6 Za a kuma kira ku firistocin Ubangiji, za a kira ku masu hidimar Allahnmu. Za ku ci wadatar waɗansu al’ummai, kuma a cikin dukiyarsu za ku yi taƙama.
Mais vous, vous serez appelés les Sacrificateurs de l'Eternel, et on vous nommera les Ministres de notre Dieu; vous mangerez les richesses des nations, et vous vous vanterez de leur gloire.
7 A maimakon kunyarsu mutanena za su sami rabi riɓi biyu, a maimakon wulaƙanci za su yi farin ciki cikin gādonsu; ta haka za su gāji rabo riɓi biyu a ƙasarsu, da kuma madawwamin farin ciki zai zama nasu.
Au lieu de la honte que vous avez eue [les nations en auront] le double, et elles crieront tout haut [que] la confusion est leur portion; c'est pourquoi ils posséderont le double en leur pays, [et] auront une joie éternelle.
8 “Gama ni, Ubangiji, ina ƙaunar adalci; na ƙi fashi da aikata laifi. Cikin adalcina zan sāka musu in kuma yi madawwamin alkawari da su.
Car je suis l'Eternel, qui aime le jugement, [et] qui hais la rapine pour l'holocauste; j'établirai leur œuvre dans la vérité, et je traiterai avec eux une alliance éternelle.
9 Za a san da zuriyarsu a cikin al’ummai’ya’yansu kuma a cikin mutane. Dukan waɗanda suka gan su za su san cewa su mutane ne da Ubangiji ya sa wa albarka.”
Et leur race sera connue entre les nations, et ceux qui seront sortis d'eux, [seront connus] parmi les peuples; tous ceux qui les verront connaîtront qu'ils sont la race que l'Eternel aura bénie.
10 Ina jin daɗi ƙwarai a cikin Ubangiji; raina yana farin ciki a cikin Allahna. Gama ya suturce ni da rigunan ceto ya yi mini ado da rigar adalci, yadda ango yakan yi wa kansa ado kamar firist kamar kuma yadda amarya takan sha ado da duwatsunta masu daraja.
Je me réjouirai extrêmement en l'Eternel, et mon âme s'égayera en mon Dieu; car il m'a revêtu des vêtements du salut, et m'a couvert du manteau de la justice, comme un époux qui se pare de magnificence, et comme une épouse qui s'orne de ses joyaux.
11 Gama kamar yadda ƙasa takan sa tsire-tsire su tohu lambu kuma ya sa iri ya yi girma, haka Ubangiji Mai Iko Duka zai sa adalci da yabo su tsiro a gaban dukan al’ummai.
Car comme la terre pousse son germe, et comme un jardin fait germer les choses qui y sont semées, ainsi le Seigneur l'Eternel fera germer la justice, et la louange en la présence de toutes les nations.

< Ishaya 61 >