< Ishaya 61 >
1 Ruhun Ubangiji Mai Iko Duka yana a kaina, domin Ubangiji ya shafe ni domin in yi wa’azi labari mai daɗi ga matalauta. Ya aiko ni in warkar da waɗanda suka karai a zuci, don in yi shelar’yanci don ɗaurarru in kuma kunce’yan kurkuku daga duhu
The Spirit of the Lord is upon me, for the Lord has anointed me. He has sent me to bring good news to the meek, so as to heal the contrite of heart, to preach leniency to captives and release to the confined,
2 don in yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji da kuma ranar ɗaukan fansar Allahnmu, don in ta’azantar da dukan waɗanda suke makoki,
and so to proclaim the acceptable year of the Lord and the day of vindication of our God: to console all who are mourning,
3 in tanada wa waɗanda suke baƙin ciki a Sihiyona, in maido musu rawani mai kyau a maimako na toka, man murna a maimako na makoki, da kuma rigar yabo a maimako na ruhun fid da zuciya. Za a ce da su itatuwan oak na adalci, shukin Ubangiji don bayyana darajarsa.
to take up the mourners of Zion and to give them a crown in place of ashes, an oil of joy in place of mourning, a cloak of praise in place of a spirit of grief. And there, they shall be called the strong ones of justice, the planting of the Lord, unto glorification.
4 Za su sāke gina kufai na dā su raya wurare da aka lalace tun da daɗewa; za su sabunta biranen da aka rurrushe da aka lalace tun zamanai masu yawa da suka wuce.
And they will rebuild the deserted places of past ages, and they will raise up the ruins of antiquity, and they will repair the desolate cities, which had been dissipated for generation after generation.
5 Baƙi za su yi kiwon garkunanki; baƙi za su yi miki noman gonaki da gonakin inabinki.
And foreigners will stand up and will pasture your flocks. And the sons of sojourners will be your farmers and the workers of your vineyards.
6 Za a kuma kira ku firistocin Ubangiji, za a kira ku masu hidimar Allahnmu. Za ku ci wadatar waɗansu al’ummai, kuma a cikin dukiyarsu za ku yi taƙama.
But you yourselves will be called the priests of the Lord. It will be said to you, “You are the ministers of our God.” You will eat from the strength of the Gentiles, and you will pride yourself on their glory.
7 A maimakon kunyarsu mutanena za su sami rabi riɓi biyu, a maimakon wulaƙanci za su yi farin ciki cikin gādonsu; ta haka za su gāji rabo riɓi biyu a ƙasarsu, da kuma madawwamin farin ciki zai zama nasu.
Instead of your double confusion and shame, they will praise their portion. Because of this, they will possess double in their land. Everlasting joy will be for them.
8 “Gama ni, Ubangiji, ina ƙaunar adalci; na ƙi fashi da aikata laifi. Cikin adalcina zan sāka musu in kuma yi madawwamin alkawari da su.
For I am the Lord, who loves judgment and who holds hatred for robbery within a burnt offering. And I will turn their work into truth, and I will forge a perpetual covenant with them.
9 Za a san da zuriyarsu a cikin al’ummai’ya’yansu kuma a cikin mutane. Dukan waɗanda suka gan su za su san cewa su mutane ne da Ubangiji ya sa wa albarka.”
And they will know their offspring among the nations, and their progeny in the midst of the peoples. All who see them will recognize them: that these are the offspring whom the Lord has blessed.
10 Ina jin daɗi ƙwarai a cikin Ubangiji; raina yana farin ciki a cikin Allahna. Gama ya suturce ni da rigunan ceto ya yi mini ado da rigar adalci, yadda ango yakan yi wa kansa ado kamar firist kamar kuma yadda amarya takan sha ado da duwatsunta masu daraja.
I will rejoice greatly in the Lord, and my soul will exult in my God. For he has clothed me with the vestments of salvation, and he has wrapped me in the clothing of justice, like a groom arrayed with a crown, and like a bride adorned with her jewels.
11 Gama kamar yadda ƙasa takan sa tsire-tsire su tohu lambu kuma ya sa iri ya yi girma, haka Ubangiji Mai Iko Duka zai sa adalci da yabo su tsiro a gaban dukan al’ummai.
For as the earth brings forth its seedlings and the garden produces its seeds, so will the Lord God bring forth justice and praise in the sight of all the nations.