< Ishaya 60 >
1 “Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
Statt upp, var ljus; ty ditt ljus kommer, och Herrans härlighet går upp öfver dig.
2 Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
Ty si, mörker öfvertäcker jordena, och mörkhet folken; men öfver dig uppgår Herren, och hans härlighet skall synas öfver dig.
3 Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
Och Hedningarna skola vandra i dino ljuse, och Konungar uti skenet, som uppgår öfver dig.
4 “Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
Lyft upp din ögon, och se omkring dig; desse alle församlade komma till dig; dine söner skola komma fjerranefter, och dina döttrar vid sidona uppfödda varda.
5 Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
Då skall du se dina lust, och utbrista, och ditt hjerta skall förundra och utvidga sig, när den stora hopen vid hafvet vänder sig till dig, och Hedningarnas magt kommer till dig.
6 Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
Ty de månge cameler skola öfvertäcka dig, de löpare af Midian och Epha. Af Saba skola de alle komma, guld och rökelse föra, och Herrans lof förkunna.
7 Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
Alle hjordar i Kedar skola till dig församlade varda, och Nebajoths bockar skola tjena dig; de skola uppå mitt tacknämliga altare offrade varda; ty jag vill pryda mins härlighets hus.
8 “Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
Hvilke äro de som flyga såsom skyar, och såsom dufvor till deras fenster?
9 Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
Öarna förbida mig, och skeppen i hafvet för långan tid, att de skola hafva din barn fram ifrå fjerran, samt med deras silfver och guld, Herrans dins Guds Namne, och den Heliga i Israel, den dig härligan gjort hafver.
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
Främmande skola bygga dina murar, och deras Konungar skola tjena dig; ty uti mine vrede hafver jag slagit dig, och i mine nåd förbarmar jag mig öfver dig.
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
Och dine portar skola städse öppne stå, hvarken dag eller natt tillslutne varda, att Hedningarnas magt skall till dig hafd varda, och deras Konungar tillförde varda.
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
Ty hvilke Hedningar eller Konungarike icke vilja tjena dig, de skola förgås, och Hedningarna förödde blifva.
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
Libanons härlighet skall till dig komma; furu, bok och buxbom tillsammans, till att bepryda mins helgedoms rum; ty jag vill mina fötters rum härligit göra.
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Skola ock de, som dig undertryckt hafva, bugande komma till dig, och alle de, som dig försmädat hafva, skola nederfalla till dina fötter, och skola kalla, dig en Herrans stad, ett Zion dens Heligas i Israel.
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
Ty derföre, att du hafver varit öfvergifven och förhatad, der ingen gick, vill jag göra dig till härlighet evinnerliga, och till glädje utan ända;
16 Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
Så att du skall suga mjölk af Hedningomen, och Konungabröst skola dig suga gifva; på det du skall förnimma, att jag, Herren, är din Frälsare, och jag, den mägtiga i Jacob, är din förlossare.
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
Jag vill låta komma guld för koppar, och silfver för jern, och koppar för trä, och jern för sten; och vill så görat, att dine föreståndare skola, frid lära, och dine skaffare predika rättfärdighet.
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
Man skall ingen orätt mer höra uti ditt land, ej heller skada eller förderf uti dina gränsor; utan dine murar skola heta salighet, och dine portar lof.
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
Solen skall icke mer skina dig om dagen, och månens sken skall icke mer lysa dig; utan Herren varder ditt eviga ljus, och din Gud skall din pris vara.
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
Din sol skall icke mer nedergå, eller din måne tappa sitt sken; ty Herren skall vara ditt eviga ljus, och dine sorgedagar skola en ända hafva.
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
Och ditt folk skola allesamman vara rättfärdige, och skola besitta jordena evinnerliga; såsom de der mine planterings qvist, och mina händers verk äro, till pris.
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”
Utaf dem minsta skola varda tusende, och utaf dem ringesta ett mägtigt folk; Jag, Herren, vill detta i sinom tid snarliga uträtta.