< Ishaya 60 >

1 “Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
برخیز و درخشان شو زیرا نور تو آمده و جلال خداوند بر تو طالع گردیده است.۱
2 Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
زیرا اینک تاریکی جهان را و ظلمت غلیظ طوایف را خواهد پوشانید اما خداوند بر توطلوع خواهد نمود و جلال وی بر تو ظاهرخواهد شد.۲
3 Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
و امت‌ها بسوی نور تو و پادشاهان بسوی درخشندگی طلوع تو خواهند آمد.۳
4 “Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
چشمان خود را به اطراف خویش برافراز و ببین که جمیع آنها جمع شده، نزد تو می‌آیند. پسرانت از دور خواهند آمد و دخترانت را در آغوش خواهند‌آورد.۴
5 Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
آنگاه خواهی دید و خواهی درخشید و دل تو لرزان شده، وسیع خواهد گردید، زیرا که توانگری دریا بسوی تو گردانیده خواهد شد و دولت امت‌ها نزد تو خواهد آمد.۵
6 Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
کثرت شتران و جمازگان مدیان و عیفه تو راخواهند پوشانید. جمیع اهل شبع خواهند آمد وطلا و بخور آورده، به تسبیح خداوند بشارت خواهند داد.۶
7 Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
جمیع گله های قیدار نزد تو جمع خواهند شد و قوچهای نبایوت تو را خدمت خواهند نمود. به مذبح من با پذیرایی برخواهندآمد و خانه جلال خود را زینت خواهم داد.۷
8 “Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
اینها کیستند که مثل ابر پرواز می‌کنند ومانند کبوتران بر وزنهای خود؟۸
9 Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
به درستی که جزیره‌ها و کشتیهای ترشیش اول انتظار مراخواهند کشید تا پسران تو را از دور و نقره وطلای ایشان را با ایشان بیاورند، به جهت اسم یهوه خدای تو و به جهت قدوس اسرائیل زیرا که تو را زینت داده است.۹
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
و غریبان، حصارهای تو را بنا خواهند نمود و پادشاهان ایشان تو راخدمت خواهند کرد زیرا که در غضب خود تو رازدم لیکن به لطف خویش تو را ترحم خواهم نمود.۱۰
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
دروازه های تو نیز دائم باز خواهد بود وشب و روز بسته نخواهد گردید تا دولت امت‌ها رانزد تو بیاورند و پادشاهان ایشان همراه آورده شوند.۱۱
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
زیرا هر امتی و مملکتی که تو را خدمت نکند تلف خواهد شد و آن امت‌ها تمام هلاک خواهند گردید.۱۲
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
جلال لبنان با درختان صنوبر و کاج و چناربا هم برای تو آورده خواهند شد تا مکان مقدس مرا زینت دهند و جای پایهای خود را تمجیدخواهم نمود.۱۳
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
و پسران آنانی که تو را ستم می رسانند خم شده، نزد تو خواهند آمد و جمیع آنانی که تو را اهانت می‌نمایند نزد کف پایهای توسجده خواهند نمود و تو را شهر یهوه و صهیون قدوس اسرائیل خواهند نامید.۱۴
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
به عوض آنکه تو متروک و مبغوض بودی و کسی از میان تو گذرنمی کرد. من تو را فخر جاودانی و سرور دهرهای بسیار خواهم گردانید.۱۵
16 Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
و شیر امت‌ها را خواهی مکید و پستانهای پادشاهان را خواهی مکید وخواهی فهمید که من یهوه نجات‌دهنده تو هستم و من قدیر اسرائیل، ولی تو می‌باشم.۱۶
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
به‌جای برنج، طلا خواهم آورد و به‌جای آهن، نقره و به‌جای چوب، برنج و به‌جای سنگ، آهن خواهم آورد و سلامتی را ناظران تو و عدالت را حاکمان تو خواهم گردانید.۱۷
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
و بار دیگر ظلم در زمین توو خرابی و ویرانی در حدود تو مسموع نخواهدشد و حصارهای خود را نجات و دروازه های خویش را تسبیح خواهی نامید.۱۸
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
و بار دیگرآفتاب در روز نور تو نخواهد بود و ماه بادرخشندگی برای تو نخواهد تابید زیرا که یهوه نور جاودانی تو و خدایت زیبایی تو خواهد بود.۱۹
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
و بار دیگر آفتاب تو غروب نخواهد کرد و ماه تو زوال نخواهد پذیرفت زیرا که یهوه برای تونور جاودانی خواهد بود و روزهای نوحه گری توتمام خواهد شد.۲۰
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
و جمیع قوم تو عادل خواهند بود و زمین را تا به ابد متصرف خواهندشد. شاخه مغروس من و عمل دست من، تاتمجید کرده شوم.۲۱
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”
صغیر هزار نفر خواهد شدو حقیر امت قوی خواهد گردید. من یهوه دروقتش تعجیل در آن خواهم نمود.۲۲

< Ishaya 60 >