< Ishaya 60 >

1 “Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
Stå op, bli lys! For ditt lys kommer, og Herrens herlighet går op over dig.
2 Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
Se, mørke dekker jorden, og mulm folkene, men over dig skal Herren opgå, og over dig skal hans herlighet åpenbare sig,
3 Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
og folkeslag skal søke til ditt lys, og konger til den glans som er gått op over dig.
4 “Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
Løft dine øine og se dig omkring! De samler sig alle sammen, de kommer til dig; dine sønner skal komme fra det fjerne, og dine døtre skal bæres på armen.
5 Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
Da skal du se det og stråle av glede, og ditt hjerte skal banke og utvide sig; for havets rikdom skal vende sig til dig, folkenes gods skal komme til dig.
6 Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
Et mylder av kameler skal dekke dig, Midians og Efas kamelføll; alle sammen skal de komme fra Sjeba; gull og virak skal de føre til dig, og Herrens pris skal de forkynne.
7 Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
Alle Kedars får skal samles til dig, Nebajots værer skal tjene dig; til mitt velbehag skal de ofres på mitt alter, og min herlighets hus vil jeg herliggjøre.
8 “Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
Hvem er disse som kommer flyvende som skyer, som duer til sine dueslag?
9 Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
For på mig skal øene vente, og fremst seiler Tarsis-skibene og fører dine barn hit fra det fjerne, deres sølv og gull kommer med dem - for Herrens, din Guds navns skyld, for Israels Helliges skyld, for han herliggjør dig.
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
Og fremmede skal bygge dine murer, og deres konger skal tjene dig; i min harme har jeg slått dig, men i min nåde har jeg forbarmet mig over dig.
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
Og dine porter skal holdes åpne all tid, hverken dag eller natt skal de lukkes, så folkenes gods kan føres inn til dig, og deres konger føres med som fanger.
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
For det folk og det rike som ikke vil tjene dig, skal gå til grunne, og hedningene skal bli aldeles ødelagt.
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
Libanons herlighet skal komme til dig, både cypress og lønn og buksbom, for å pryde det sted der min helligdom er, og det sted hvor mine føtter står, vil jeg herliggjøre.
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Og barna til dem som har plaget dig, skal komme bøiede til dig, og alle de som har foraktet dig, skal kaste sig ned for dine føtter, og de skal kalle dig Herrens stad, Israels Helliges Sion.
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
I stedet for at du var forlatt og hatet, så det ikke var nogen som drog igjennem dig, vil jeg gjøre dig til en evig herlighet, en fryd for slekt efter slekt.
16 Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
Og du skal die hedningefolks melk, ja, kongers bryst skal du die, og du skal kjenne at jeg, Herren, er din frelser, og Jakobs Veldige din gjenløser.
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
I stedet for kobber vil jeg gi gull, i stedet for jern vil jeg gi sølv, i stedet for tre kobber og i stedet for sten jern, og jeg vil gjøre fred til din øvrighet og rettferdighet til din styrer.
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
Det skal ikke mere høres om vold i ditt land, ikke om hærfang og ødeleggelse innen dine landemerker, og du skal kalle frelsen dine murer og lovsangen dine porter.
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
Solen skal ikke mere være ditt lys om dagen, og månen skal ikke skinne og lyse for dig; men Herren skal være et evig lys for dig, og din Gud skal være din herlighet.
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
Din sol skal ikke mere gå ned, og din måne ikke miste sitt skinn; for Herren skal være et evig lys for dig, og din sorgs dager skal være til ende.
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
Og ditt folk - de er alle sammen rettferdige; til evig tid skal de eie landet; de er jo en kvist som jeg har plantet, et verk av mine hender til min ære.
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”
Den minste skal bli til tusen, og den ringeste til et veldig folk; jeg, Herren, jeg vil la det skje hastig, i sin tid.

< Ishaya 60 >