< Ishaya 60 >

1 “Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
Mache dich auf, werde Licht; denn dein Licht kommt, und Jehovahs Herrlichkeit ist aufgegangen über dir.
2 Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
Denn siehe, Finsternis bedeckt die Erde, und Dunkel die Volksstämme; aber über dir geht auf Jehovah, und Seine Herrlichkeit erscheint über dir.
3 Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
Und Völkerschaften werden zu deinem Lichte wandeln und Könige zum Glanze deines Aufgangs.
4 “Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
Erhebe ringsum deine Augen, und siehe, sie alle kommen zusammen, sie kommen zu dir, von ferne werden deine Söhne kommen und deine Töchter werden zur Seite von Wärterinnen herbeigetragen.
5 Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
Dann wirst du es sehen, und herbeiströmen und schauern wird dein Herz und sich erweitern, denn zu dir wird umkehren des Meeres Menge, und die Streitmacht der Völkerschaften zu dir kommen.
6 Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
Bedecken wird dich der Kamele Unzahl, Midjans und Ephahs Dromedare; sie alle kommen von Scheba, Gold und Weihrauch tragen sie und verkünden das Lob Jehovahs.
7 Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
Zu dir kommen zusammen alle Herden Kedars, dir sind zu Dienste die Widder Nebajoths und werden zum Wohlgefallen aufsteigen auf Meinem Altar, und verklären will Ich Meines Schmuckes Haus.
8 “Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
Wer sind diese, die daher wie eine dichte Wolke fliegen, und wie die Tauben zu ihren Fenstern?
9 Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
Denn auf Mich hoffen die Inseln, und zuerst die Schiffe von Tharschisch, zu bringen deine Söhne von ferne, ihr Silber und ihr Gold mit ihnen, dem Namen Jehovahs, deines Gottes, und dem Heiligen Israels; daß Er dich hat verklärt.
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
Und die Söhne des Auslandes werden deine Mauern bauen, und ihre Könige dir zu Dienste sein, denn in Meiner Entrüstung habe Ich dich geschlagen, und in Meinem Wohlgefallen deiner Mich erbarmt.
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
Und geöffnet sind deine Tore beständig, bei Tag und bei Nacht werden sie nicht geschlossen, damit man zu dir bringe der Völkerschaften Streitmacht, und ihre Könige werden herzugeleitet.
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
Denn die Völkerschaften und das Königreich, die dir nicht dienen, vergehen, und verödet werden die Völkerschaften.
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
Die Herrlichkeit des Libanon wird zu dir kommen; Tanne, Kiefer und Buchsbaum allzumal, den Ort Meines Heiligtums zu schmücken, und den Ort Meiner Füße will Ich verherrlichen.
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Und zu dir kommen niedergebeugt die Söhne derer, die dich niedergedrückt, und sie beugen sich nieder zu den Sohlen deiner Füße, alle, die dich gelästert; und nennen werden sie dich die Stadt Jehovahs, das Zion des Heiligen Israels.
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
Statt daß du warst verlassen und gehaßt, daß niemand durchging, will Ich dich machen zum ewigen Stolze, zur Freude von Geschlecht zu Geschlecht.
16 Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
Und die Milch der Völkerschaften wirst du saugen, und der Könige Brust wirst du saugen, daß du wissest, daß Ich, Jehovah, bin dein Heiland und dein Erlöser, der Gewaltige Jakobs.
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
Statt Erzes bringe Ich Gold, und statt Eisens bringe Ich Silber, und statt des Holzes Erz und statt der Steine Eisen, und Ich will zu deiner Obrigkeit Frieden setzten, und zu deinen Fronvögten Gerechtigkeit.
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
Nicht wird man mehr in deinem Lande von Gewalttat hören, in deinen Grenzen von Verheerung und vom Zerbrechen, und deine Mauern wirst du nennen Heil und deine Tore Lob.
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
Nicht wird die Sonne mehr bei Tag dir zum Lichte sein, noch zum Glanz der Mond dir scheinen; sondern Jehovah wird dir sein ein ewig Licht, und dein Gott zu deinem Schmuck.
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
Nicht wird mehr deine Sonne untergehen, und dein Mond sich nicht zurückziehen; denn Jehovah wird dir sein ein Licht der Ewigkeit, und die Tage deiner Trauer sind vollbracht.
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
Und all dein Volk werden Gerechte sein, ewiglich sollen sie das Land erblich besitzen, ein Reis meiner Pflanzungen sind sie, ein Werk von Meinen Händen, Mich zu verklären.
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”
Der Kleine soll zu Tausend und der Geringe zur zahlreichen Völkerschaft werden. Ich, Jehovah, werde es zu seiner Zeit beschleunigen.

< Ishaya 60 >