< Ishaya 60 >

1 “Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
Lève-toi, reçois la lumière, Jérusalem, parce qu’est venue ta lumière, et que la gloire du Seigneur sur toi s’est levée.
2 Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
Parce que voilà que les ténèbres couvriront la terre, et une obscurité, les peuples; mais sur toi se lèvera le Seigneur, et sa gloire en toi se verra.
3 Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
Et des nations marcheront à ta lumière, et des rois à la splendeur de ton lever.
4 “Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
Lève autour de toi tes yeux et vois; tous ceux-ci se sont rassemblés, ils sont venus à toi; tes fils de loin viendront, et tes filles à ton côté se lèveront.
5 Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
Alors tu verras, et tu seras dans l’abondance; ton cœur admirera, et se dilatera, quand se sera tournée vers toi la richesse de la mer, et que la force des nations sera venue à toi.
6 Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
Une inondation de chameaux te couvrira ainsi que les dromadaires de Madian et d’Epha; tous viendront de Saba, apportant de l’or et de l’encens, et publiant des louanges en l’honneur du Seigneur.
7 Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
Tout troupeau de Cédar sera rassemblé pour toi, les béliers de Nabaïoth seront employés à ton service; ils seront offerts sur mon autel d’expiation, et je glorifierai la maison de ma majesté.
8 “Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
Qui sont ceux-ci qui volent comme des nuées, et comme des colombes vers leurs demeures?
9 Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
Car les îles m’attendent, ainsi que les vaisseaux de mer, dès le principe, afin que je fasse venir tes fils de loin, leur or et leur argent avec eux, et les consacre au nom du Seigneur ton Dieu et au saint d’Israël, parce qu’il t’a glorifiée.
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
Et les fils des étrangers bâtiront des murs, et leurs rois te serviront; car dans mon indignation je t’ai frappée, et par ma réconciliation j’ai eu pitié de toi.
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
Et tes portes seront ouvertes continuellement; ni jour ni nuit elles ne seront fermées, afin que te soit apportée la force des nations, et que leurs rois te soient amenés.
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
Car la nation et le royaume qui ne te sera pas assujetti, périra; ces nations réduites en solitude seront dévastées.
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
La gloire du Liban vers toi viendra; le sapin, et le buis, et le pin serviront ensemble à orner le lieu de ma sanctification; et la place de mes pieds, je la glorifierai.
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Et ils viendront vers toi, les fils de ceux qui t’ont humiliée, et ils adoreront les traces de tes pieds, tous ceux qui te décriaient, et ils t’appelleront la cité du Seigneur, la Sion du saint d’Israël.
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
Parce que tu as été délaissée et haïe, et qu’il n’y avait personne qui te traversât, je t’établirai l’orgueil des siècles, et la joie pour toutes les générations.
16 Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
Et tu suceras le lait des nations, et de la mamelle des rois tu seras nourrie; et tu sauras que je suis le Seigneur qui te sauve, et ton rédempteur le fort de Jacob.
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
Au lieu d’airain j’apporterai de l’or, et au lieu de fer j’apporterai de l’argent; et au lieu de bois, de l’airain, et au lieu de pierre, du fer; je te donnerai pour gouvernement la paix, et pour préposés, la justice.
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
On n’entendra plus parler d’iniquité dans ta terre, de ravage et de destruction dans tes confins; et le salut occupera tes murs, et la louange tes portes.
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
Tu n’auras plus le soleil pour éclairer pendant le jour, et la clarté de la lune ne luira pas sur toi; mais le Seigneur sera ta lumière éternelle, et ton Dieu ta gloire.
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
Ton soleil ne se couchera plus, et ta lune ne diminuera pas; parce que le Seigneur sera ta lumière éternelle, et que les jours de ton deuil seront finis.
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
Quant à ton peuple, tous seront justes; pour toujours ils posséderont la terre en héritage; il sera le rejeton de ma plantation, l’œuvre de ma main pour me glorifier.
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”
Le moindre de tes citoyens en produira mille, et le plus petit une nation très puissante; moi le Seigneur, en son temps je ferai soudain cela.

< Ishaya 60 >