< Ishaya 60 >

1 “Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
Lève-toi, sois illuminée; car ta lumière est venue, et la gloire de l'Eternel s'est levée sur toi.
2 Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
Car voici, les ténèbres couvriront la terre, et l'obscurité couvrira les peuples; mais l'Eternel se lèvera sur toi, et sa gloire paraîtra sur toi.
3 Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
Et les nations marcheront à ta lumière, et les Rois à la splendeur qui se lèvera sur toi.
4 “Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
Elève tes yeux à l'environ, et regarde; tous ceux-ci se sont assemblés, ils sont venus vers toi; tes fils viendront de loin, et tes filles seront nourries par des nourriciers, [étant portées] sur les côtés.
5 Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
Alors tu verras, et tu seras éclairée, et ton cœur s'étonnera, et s'épanouira [de joie], quand l'abondance de la mer se sera tournée vers toi, et que la puissance des nations sera venue chez toi.
6 Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
Une abondance de chameaux te couvrira; les dromadaires de Madian et d'Hépha, et tous ceux de Séba viendront, ils apporteront de l'or et de l'encens, et publieront les louanges de l'Eternel.
7 Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
Toutes les brebis de Kédar seront assemblées vers toi, les moutons de Nébajoth seront pour ton service; ils seront agréables étant offerts sur mon autel, et je rendrai magnifique la maison de ma gloire.
8 “Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
Quelles sont ces volées, épaisses comme des nuées, qui volent comme des pigeons à leurs trous?
9 Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
Car les Iles s'attendront à moi, et les navires de Tarsis les premiers, afin d'amener tes fils de loin, avec leur argent et leur or, pour l'amour du Nom de l'Eternel ton Dieu, et du Saint d'Israël, parce qu'il t'aura glorifiée.
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
Et les fils des étrangers rebâtiront tes murailles, et leurs Rois seront employés à ton service; car je t'ai frappée en ma fureur, mais j'ai eu pitié de toi au temps de mon bon plaisir.
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
Tes portes aussi seront continuellement ouvertes, elles ne seront fermées ni nuit ni jour, afin que les forces des nations te soient amenées, et que leurs Rois y soient conduits.
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
Car la nation et le Royaume qui ne te serviront point, périront; et ces nations-là seront réduites en une entière désolation.
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
La gloire du Liban viendra vers toi, le sapin, l'orme, et le buis ensemble, pour rendre honorable le lieu de mon Sanctuaire; et je rendrai glorieux le lieu de mes pieds.
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Même les enfants de ceux qui t'auront affligée viendront vers toi en se courbant; et tous ceux qui te méprisaient se prosterneront à tes pieds, et t'appelleront, La ville de l'Eternel, la Sion du Saint d'Israël.
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
Au lieu que tu as été délaissée et haïe, tellement qu'il n'y avait personne qui passât [parmi toi], je te mettrai dans une élévation éternelle, [et] dans une joie qui sera de génération en génération.
16 Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
Et tu suceras le lait des nations, et tu suceras la mamelle des Rois, et tu sauras que je suis l'Eternel ton Sauveur, et ton Rédempteur, le Puissant de Jacob.
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
Je ferai venir de l'or au lieu de l'airain, et je ferai venir de l'argent au lieu du fer, et de l'airain au lieu du bois, et du fer au lieu des pierres; et je ferai que la paix te gouvernera, et que tes exacteurs ne seront que justice.
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
On n'entendra plus parler de violence en ton pays, ni de dégât, ni de calamité en tes contrées, mais tu appelleras tes murailles, Salut, et tes portes, Louange.
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
Tu n'auras plus le soleil pour la lumière du jour, et la lueur de la lune ne t'éclairera plus; mais l'Eternel te sera pour lumière éternelle, et ton Dieu pour ta gloire.
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
Ton soleil ne se couchera plus, et ta lune ne se retirera plus, car l'Eternel te sera pour lumière perpétuelle, et les jours de ton deuil seront finis.
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
Et quant à ton peuple, ils seront tous justes; ils posséderont éternellement la terre; [savoir] le germe de mes plantes, l'œuvre de mes mains, pour y être glorifié.
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”
La petite [famille] croîtra jusqu'à mille [personnes], et la moindre deviendra une nation forte. Je suis l'Eternel, je hâterai ceci en son temps.

< Ishaya 60 >