< Ishaya 60 >

1 “Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
[You people of] Jerusalem [PRS], stand up! Yahweh has done glorious things for you, and he has acted powerfully for you; so show others that he is very great!
2 Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
[But spiritual] darkness has covered [all the other people-groups on] the earth, complete darkness, but Yahweh will show you how great he is, and other people will also see it.
3 Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
By seeing what he has done for you, [people of all] people-groups will see that he is very great, and kings will come to see the wonderful things that have happened to you.
4 “Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
[Yahweh says], “Look around and you will see the people who will be returning from (exile/countries to which they have been forced to go)! Your sons will come from distant countries; others will carry your [little] daughters home.
5 Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
When you look at this happening, you will be very joyful [DOU], because people will bring valuable goods to you [from all around the world]. They will bring in ships valuable things from [many] nations.
6 Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
People will [also] bring valuable goods to you on herds/caravans of camels: Camels from the Midian and Ephah [areas of northern Arabia]. And from Sheba [in southern Arabia] they will come, bringing gold and frankincense; they will all come to praise [me], Yahweh.
7 Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
They will bring flocks [of sheep and goats] from Kedar [in northern Arabia and give them] to you. [They will bring] [PRS] rams from Nebaioth for you [to sacrifice] on my altars, and I will accept them [happily]. [At that time] I will cause my temple to be very beautifully decorated.
8 “Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
And what are those things that are moving swiftly like [SIM] clouds? They resemble [SIM] doves [returning] to their nests.
9 Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
But they are really ships from Tarshish that are bringing your people back here. When your people come, they will bring with them [all] the valuable possessions that they have acquired, and [they will do that] to honor [me], Yahweh, your God, the Holy One of Israel, because I will have greatly honored you.
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
Foreigners will [come and] rebuild the walls of your [cities], and their kings will serve/help you. Although I punished you because I was angry with you, these things will happen now because I will act mercifully toward you because I am kind.
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
The gates of your [cities] will be open during the day and [also] during the night, in order that people will be able to bring into your cities valuable things from [many] countries, with their kings being led to you in the processions.
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
And the kingdoms and nations whose [people] refuse to allow you to rule them will be completely destroyed [DOU].
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
The glorious/beautiful things in Lebanon will be brought to you— [lumber from] cypress [trees] and fir [trees] and pine [trees]— to be used to make my temple beautiful. When that is done, my temple [MTY] will [truly] be glorious!
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
The descendants of those who (oppressed you/treated you cruelly) will come and bow down to you; those who despised you will prostrate themselves in front of your feet. They will say that your city on Zion Hill is the City of Yahweh, where the Holy One of Israel lives.
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
Previously everyone hated you and ignored you, but now your [city] will be majestic/honored forever; and [I will cause you to be] joyful forever.
16 Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
People of all nations and their kings will gladly bring [MET] their wealth to you. And [when that happens], you will realize that I truly am Yahweh, the one who saves you and rescues you [from your enemies], and that I am the mighty one to whom you Israeli people belong.
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
Instead of [metals that are not valuable, like] bronze and iron, I will bring to you silver and gold. Instead of wood and stones, I will bring you bronze and iron [for your buildings]. There will be peace in your country, and your rulers will do what is fair/just.
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
People in your country will no longer act violently, and people will no longer destroy your land and cause it to become desolate/ruined. The people in the city will be safe, and everyone there will praise me [MTY].
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
And you will no longer need the sun and moon to give you light, because [I], Yahweh, will give you more light [than the sun and moon]; I will be a glorious light for you forever.
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
[It will seem as though] the sun and moon will always be shining [LIT], because [I], Yahweh, will be an everlasting light for you. You will never again be sad [because of things that happen to you].
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
Your people will all be righteous, and they will occupy the land forever, because I myself have put you there [like people plant trees] [MET] in order that you will show others that I am very great.
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”
At that time, the [groups that are] very small now will become [very large] clans, and small clans will become great nations. [All those things will happen because], I, Yahweh, will cause them to happen at the right time.”

< Ishaya 60 >