< Ishaya 60 >

1 “Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
Arise, shine! for thy light is come, And the glory of Jehovah is risen upon thee.
2 Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
For, behold, darkness shall cover the earth, And gross darkness the nations; But upon thee shall Jehovah arise, And his glory shall be seen upon thee.
3 Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
Nations shall come to thy light, And kings to the brightness that riseth upon thee.
4 “Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
Lift up thine eyes round about and see! They all gather themselves together, and come to thee; Thy sons come from afar, And thy daughters are carried at thy side.
5 Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
Then shalt thou see, and be bright with joy; Thy heart shall throb, and swell with delight, When the riches of the sea shall be turned toward thee, And the wealth of the nations shall come to thee.
6 Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
A multitude of camels shall cover thee, Dromedaries from Midian and Ephah; From Sheba shall they all come. Gold and frankincense shall they bring, And proclaim the praises of Jehovah.
7 Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
All the flocks of Kedar shall be gathered to thee, And the rams of Nebaioth shall minister to thee; They shall ascend mine altar, an acceptable offering, And my glorious house I will adorn.
8 “Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
Who are these that fly like clouds, And like doves to their habitations?
9 Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
Behold, the distant coasts shall wait for me, And the ships of Tarshish among the first, To bring thy sons from afar, And their silver and their gold with them, Because of the name of Jehovah thy God, Of the Holy One of Israel, for he glorifieth thee.
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
The sons of the stranger shall build up thy walls, And their kings shall minister to thee; For in my wrath I smote thee, But in my mercy will I have pity upon thee.
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
Thy gates shall be open continually; They shall not be shut by day or by night, That the treasures of the nations may be brought to thee, And that their kings may come with their retinues.
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
For that nation and that kingdom Which will not serve thee shall perish; Yea, those nations shall be utterly destroyed.
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
The glory of Lebanon shall come to thee, The cypress, the plane-tree, and the larch together, To adorn the place of my sanctuary, That I may make the place where my feet rest glorious.
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
The sons of thine oppressors shall come bending before thee; They that despised thee shall fall down at thy feet; And they shall call thee the city of Jehovah, The Zion of the Holy One of Israel.
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
Instead of being forsaken and hated, So that no one passed through thee, I will make thee an everlasting glory; The joy of many generations.
16 Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
Thou shalt also suck the milk of the nations, And be nursed from the breast of kings; And thou shalt know that I, Jehovah, am thy saviour, That thy redeemer is the Mighty One of Jacob.
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
Instead of brass will I bring gold; And instead of iron will I bring silver, And instead of wood, brass, And instead of stones, iron; I will make thine officers peace, And thy magistrates righteousness.
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
Violence shall no more be heard in thy land, Wasting or destruction within thy borders; Thou shalt call thy walls Salvation, And thy gates Praise.
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
No more shall the sun be thy light by day, Nor with her brightness shall the moon enlighten thee: But Jehovah shall be to thee an everlasting light, And thy God thy glory.
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
Thy sun shall no more go down, Neither shall thy moon be hid; For Jehovah shall be thine everlasting light, And the days of thy mourning shall be ended.
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
Thy people shall be all righteous; Forever shall they possess the land, The scion of my planting, The work of my hands, that I may be glorified.
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”
The little one shall become a thousand, And the small one a strong nation; I, Jehovah, will hasten it in its time.

< Ishaya 60 >