< Ishaya 60 >

1 “Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
Arise, O Ierusalem: be bright, for thy light is come, and the glorie of the Lord is risen vpon thee.
2 Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
For beholde, darkenesse shall couer the earth, and grosse darkenesse the people: but the Lord shall arise vpon thee, and his glory shall be seene vpon thee.
3 Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
And the Gentiles shall walke in thy light, and Kings at the brightnesse of thy rising vp.
4 “Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
Lift vp thine eyes round about, and beholde: all these are gathered, and come to thee: thy sonnes shall come from farre, and thy daughters shalbe nourished at thy side.
5 Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
Then thou shalt see and shine: thine heart shall be astonied and enlarged, because the multitude of the sea shalbe conuerted vnto thee, and the riches of the Gentiles shall come vnto thee.
6 Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
The multitude of camels shall couer thee: and the dromedaries of Midian and of Ephah: all they of Sheba shall come: they shall bring golde and incense, and shewe foorth the prayses of the Lord.
7 Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
All the sheepe of Kedar shall be gathered vnto thee: the rammes of Nebaioth shall serue thee: they shall come vp to bee accepted vpon mine altar: and I will beautifie the house of my glorie.
8 “Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
Who are these that flee like a cloude, and as the doues to their windowes?
9 Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
Surely the yles shall waite for mee, and the shippes of Tarshish, as at the beginning, that they may bring thy sonnes from farre, and their siluer, and their golde with them, vnto the Name of the Lord thy God, and to the Holy one of Israel, because he hath glorified thee.
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
And the sonnes of strangers shall builde vp thy walles, and their Kings shall minister vnto thee: for in my wrath I smote thee, but in my mercie I had compassion on thee.
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
Therefore thy gates shalbe open continually: neither day nor night shall they be shutte, that men may bring vnto thee the riches of the Gentiles, and that their Kings may be brought.
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
For the nation and the kingdome, that will not serue thee, shall perish: and those nations shalbe vtterly destroyed.
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
The glory of Lebanon shall come vnto thee, the firre tree, the elme and the boxe tree together, to beautifie the place of my Sanctuarie: for I will glorifie the place of my feete.
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
The sonnes also of them that afflicted thee, shall come and bowe vnto thee: and all they that despised thee, shall fall downe at the soles of thy feete: and they shall call thee, The citie of the Lord, Zion of the Holy one of Israel.
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
Where as thou hast bene forsaken and hated: so that no man went by thee, I will make thee an eternall glorie, and a ioye from generation to generation.
16 Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
Thou shalt also sucke ye milke of the Gentiles, and shalt sucke the breastes of Kings: and thou shalt know, that I the Lord am thy Sauiour, and thy Redeemer, the mightie one of Iaakob.
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
For brasse will I bring golde, and for yron will I bring siluer, and for wood brasse, and for stones yron. I will also make thy gouernement peace, and thine exactours righteousnesse.
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
Violence shall no more be heard of in thy land, neither desolation, nor destruction within thy borders: but thou shalt call saluation, thy walles, and praise, thy gates.
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
Thou shalt haue no more sunne to shine by day, neither shall the brightnesse of the moone shine vnto thee: for the Lord shall be thine euerlasting light, and thy God, thy glorie.
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
Thy sunne shall neuer goe downe, neither shall thy moone be hid: for the Lord shalbe thine euerlasting light, and the dayes of thy sorowe shalbe ended.
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
Thy people also shalbe all righteous: they shall possesse the land for euer, the grasse of my planting shalbe the worke of mine handes, that I may be glorified.
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”
A litle one shall become as a thousande, and a small one as a strong nation: I the Lord wil hasten it in due time.

< Ishaya 60 >