< Ishaya 60 >

1 “Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
Stand up and shine, for your light has come; the glory of the Lord has risen on you.
2 Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
Even though darkness covers the earth, and deep darkness covers the people, the Lord has risen to shine on you, and his glory appears over you.
3 Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
Nations will come to your light, and kings will come to the brightness of your shining dawn.
4 “Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
Look all around you, and see everyone gathering and coming to you—your sons returning from far away, your young daughters being carried on the hip.
5 Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
Then you will see and shine brilliantly, your heart will beat wildly for joy, for the riches that cross the sea, the wealth of the nations, will be brought to you.
6 Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
Long caravans of camels will cover the land, young camels of Midian and Ephah. All the people of Sheba will come to you carrying gold and frankincense, shouting praises to the Lord.
7 Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
All the flocks of Kedar will be brought to you, the rams of Nebaioth will be placed at your disposal. I will accept them as they are sacrificed on my altar, and I will glorify the Temple where I'm honored.
8 “Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
What are these flying like a cloud, flying like pigeons returning to their roost?
9 Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
Coming from the islands that trust in me, these are ships led by those of Tarshish, bringing your children home from far away, carrying with them silver and gold. They come to honor of the Lord your God, the Holy One of Israel, for he has made you glorious.
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
Foreigners will rebuild your walls, and their kings will work for you. Even though I did hit you when I was angry with you, now I will be kind and merciful to you.
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
Your gates will always be kept open. They won't ever be shut, day or night, so the wealth of the nations can be brought to you, with their kings being led along in a procession.
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
Any nation or kingdom that does not serve you will be completely destroyed.
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
The glory of Lebanon will come to you: cedars, acacias, and myrtle trees, to make my Temple beautiful and to honor the place I choose to live.
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
The children of those who persecuted you will come and bow before you; everyone who looked down on you will bow down at your feet and will call you the City of the Lord, Zion of the Holy One of Israel.
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
Once you were abandoned and despised, somewhere people didn't go, but now I will make you a place to be proud of forever, a joy to every generation.
16 Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
Nations will provide you with what you need, kings will take care of you as if you were their own children. You will know that I, the Lord, am your Savior and Redeemer, the Mighty One of Jacob.
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
I will bring you gold instead of bronze, silver instead of iron, bronze instead of wood, and iron instead of stone. I will appoint Peace as your watchman, and Goodness as your leader.
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
There won't be any more violence in your land, no more devastation and destruction within your borders. You will call your walls Salvation, and your gates Praise.
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
You won't need the light of the sun during the day, or the light of the moon at night, for the Lord your God will be your everlasting light, and your God will be your glory.
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
Your sun will never set, and your moon will never wane, for the Lord will be your everlasting light, and your time of mourning will end.
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
All your people will be good, and they will own the land forever. They are the shoot I have planted with my hands, and they will reveal my glory.
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”
The smallest of your families will increase to a thousand, and the most insignificant will become a great nation. I am the Lord; at the right time I will do this quickly.

< Ishaya 60 >