< Ishaya 60 >

1 “Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
Arise, be enlightened, O Jerusalem: for thy light is come, and the glory of the Lord is risen upon thee.
2 Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
For behold darkness shall cover the earth, and a mist the people: but the Lord shall arise upon thee, and his glory shall be seen upon thee.
3 Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
And the Gentiles shall walk in thy light, and kings in the brightness of thy rising.
4 “Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
Lift up thy eyes round about, and see: all these are gathered together, they are come to thee: thy sons shall come from afar, and thy daughters shall rise up at thy side.
5 Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
Then shalt thou see, and abound, and thy heart shall wonder and be enlarged, when the multitude of the sea shall be converted to thee, the. strength of the Gentiles shall come to thee.
6 Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
The multitude of camels shall cover thee, the dromedaries of Madian and Epha: all they from Saba shall come, bringing gold and frankincense: and shewing forth praise to the Lord.
7 Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
All the flocks of Cedar shall be gathered together unto thee, the rams of Nabaioth shall minister to thee: they shall be offered upon my acceptable altar, and I will glorify the house of my majesty.
8 “Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
Who are these, that fly as clouds, and as doves to their windows?
9 Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
For, the islands wait for me, and the ships of the sea in the beginning: that I may bring thy sons from afar: their silver, and their gold with them, to the name of the Lord thy God, and to the Holy One of Israel, because he hath glorified thee.
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
And the children of strangers shall build up thy walls, and their kings shall minister to thee: for in my wrath have I struck thee, and in my reconciliation have I had mercy upon thee.
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
And thy gates shall be open continually: they shall not be shut day nor night, that the strength of the Gentiles may be brought to thee, and their kings may be brought.
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
For the nation and the kingdom that will not serve thee, shall perish: and the Gentiles shall be wasted with desolation.
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
The glory of Libanus shall come to thee, the Ar tree, and the box tree, and the pine tree together, to beautify the place of my sanctuary: and I will glorify the place of my feet.
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
And the children of them that afflict thee, shall come bowing down to thee, and all that slandered thee shall worship the steps of thy feet, and shall call thee the city of the Lord, the Sion of the Holy One of Israel.
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
Because thou wast forsaken, and hated, and there was none that passed through thee, I will make thee to be an everlasting glory, a joy unto generation and generation:
16 Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
And thou shalt suck the milk of the Gentiles, and thou shalt be nursed with the breasts of kings: and thou shalt know that I am the Lord thy Saviour, and thy Redeemer, the Mighty One of Jacob.
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
For brass I will bring gold, and for iron I will bring silver: and for wood brass, and for stones iron: and I will make thy visitation peace, and thy overseers justice.
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
Iniquity shall no more be heard in thy land, wasting nor destruction in thy borders, and salvation shall possess thy walls, and praise thy gates.
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
Thou shalt no more have the sun for thy light by day, neither shall the brightness of the moon enlighten thee: but the Lord shall be unto thee for an everlasting light, and thy God for thy glory.
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
Thy sun shall go down no more, and thy moon shall not decrease: for the Lord shall be unto thee for an everlasting light, and the days of thy mourning shall be ended.
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
And thy people shall be all just, they shall inherit the land for ever, the branch of my planting, the work of my hand to glorify me.
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”
The least shall become a thousand, and a little one a most strong nation: I the Lord will suddenly do this thing in its time.

< Ishaya 60 >