< Ishaya 60 >

1 “Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
Rise up to be illuminated, O Jerusalem! For your light has arrived, and the glory of the Lord has risen over you.
2 Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
For behold, darkness will cover the earth, and thick darkness will cover the peoples. Then the Lord will rise above you, and his glory will be seen in you.
3 Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
And the nations will walk in your light, and the kings will walk by the splendor of your rising.
4 “Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
Lift up your eyes all around and see! All these have been gathered together; they have arrived before you. Your sons will arrive from far away, and your daughters will rise up from your side.
5 Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
Then you will see, and you will overflow, and your heart will be amazed and expanded. When the multitude of the sea will have been converted to you, the strength of the nations will approach you.
6 Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
A multitude of camels will inundate you: the dromedaries from Midian and Ephah. All those from Sheba will arrive, carrying gold and frankincense, and announcing praise to the Lord.
7 Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
All the flocks of Kedar will be gathered together before you; the rams of Nebaioth will minister to you. They will be offered upon my pleasing altar, and I will glorify the house of my majesty.
8 “Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
Who are these ones, who fly like the clouds and like doves to their windows?
9 Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
For the islands await me, and the ships of the sea in the beginning, so that I may lead your sons from far away, their silver and their gold with them, to the name of the Lord your God and to the Holy One of Israel. For he has glorified you.
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
And the sons of sojourners will build up your walls, and their kings will minister to you. For in my wrath, I have struck you. And in my reconciliation, I have taken pity on you.
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
And your gates will be open continually. They will not be closed day or night, so that the strength of the nations may be brought before you, and their kings may be lead in.
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
For the nation and the kingdom that will not serve you will perish. And the Gentiles will be devastated by solitude.
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
The glory of Lebanon will arrive before you, the fir tree and the box tree and the pine tree together, to adorn the place of my sanctification. And I will glorify the place of my feet.
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
And the sons of those who humiliate you will approach and will bow down before you. And all who detract you will reverence the path of your feet. And they will call you the City of the Lord, the Zion of the Holy One of Israel.
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
For though you were forsaken, and held in hatred, and there was no one who would pass near you, I will establish you as an everlasting glory, as a gladness from generation to generation.
16 Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
And you will drink the milk of the Gentiles, and you will be nursed at the breasts of kings, and you will know that I am the Lord, your Savior and your Redeemer, the Strong One of Jacob.
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
In exchange for brass, I will bring gold; and in exchange for iron, I will bring silver; and for wood, brass; and for stones, iron. And I will make your visitation into peace, and your leaders into justice.
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
Iniquity will no longer be heard in your land, nor devastation and destruction in your borders. And salvation will occupy your walls, and praise will occupy your gates.
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
The sun will no longer be your light by day, nor will the brightness of the moon illuminate you. Instead, the Lord will be an everlasting light for you, and your God will be your glory.
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
Your sun will no longer set, and your moon will not diminish. For the Lord will be an everlasting light for you, and the days of your mourning will be completed.
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
And your people will all be just. They will inherit the earth in perpetuity, the seedling of my planting, the work of my hand, so as to glorify me.
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”
The least will become a thousand, and a little one will become a very strong nation. I, the Lord, will accomplish this, suddenly, in its time.

< Ishaya 60 >