< Ishaya 60 >

1 “Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
Gør dig rede, bliv Lys, thi dit Lys er kommet, HERRENS Herlighed er oprundet over dig.
2 Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
Thi se, Mørke skjuler Jorden og Dunkelhed Folkene, men over dig skal HERREN oprinde, over dig skal hans Herlighed ses.
3 Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
Til dit Lys skal Folkene vandre, og Konger til dit straalende Skær.
4 “Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
Løft Øjnene, se dig om, de samles, kommer alle til dig. Dine Sønner kommer fra det fjerne, dine Døtre bæres paa Hofte;
5 Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
da straaler dit Øje af Glæde, dit Hjerte banker og svulmer; thi Havets Skatte bliver dine, til dig kommer Folkenes Rigdom;
6 Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
Kamelernes Vrimmel skjuler dig, Midjans og Efas Foler, de kommer alle fra Saba; Guld og Røgelse bærer de og kundgør HERRENS Pris;
7 Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
alt Kedars Smaakvæg samles til dig, dig tjener Nebajots Vædre, til mit Velbehag ofres de til mig, mit Bedehus herliggøres.
8 “Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
Hvem flyver mon der som Skyer, som Duer til Dueslag?
9 Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
Det er Skibe, der kommer med Hast, i Spidsen er Tarsisskibe, for at bringe dine Sønner fra det fjerne; deres Sølv og Guld har de med til HERREN din Guds Navn, Israels Hellige, han gør dig herlig.
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
Udlændinge skal bygge dine Mure, og tjene dig skal deres Konger; thi i Vrede slog jeg dig vel, men i Naade forbarmer Jeg mig over dig.
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
Dine Porte holdes altid aabne, de lukkes hverken Dag eller Nat, at Folkenes Rigdom kan bringes dig med deres Konger som Førere.
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
Thi det Folk og Rige, som ikke tjener dig, skal gaa til Grunde, og Folkene skal lægges øde i Bund og Grund.
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
Til dig skal Libanons Herlighed komme, baade Cypresser og Elm og Gran, for at smykke min Helligdoms Sted, saa jeg ærer mine Fødders Skammel.
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Dine Undertrykkeres Sønner kommer bøjet til dig, og alle, som haaned dig, kaster sig ned for din Fod og kalder dig HERRENS By, Israels Helliges Zion.
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
Medens du før var forladt og hadet, saa ingen drog gennem dig, gør jeg dig til evig Højhed, til Glæde fra Slægt til Slægt.
16 Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
Du skal indsuge Folkenes Mælk og die Kongernes Bryst. Du skal kende, at jeg, HERREN, er din Frelser, din Genløser Jakobs Vældige.
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
Guld sætter jeg i Stedet for Kobber og Sølv i Stedet for Jern, Kobber i Stedet for Træ og Jern i Stedet for Sten. Til din Øvrighed sætter jeg Fred, til Hersker over dig Retfærd.
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
Der høres ej mer i dit Land om Uret, om Vold og Ufærd inden dine Grænser; du kalder Frelse dine Mure og Lovsang dine Porte.
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
Ej mer skal Solen være dit Lys eller Maanen Skinne for dig: HERREN skal være dit Lys for evigt, din Gud skal være din Herlighed.
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
Din Sol skal ej mer gaa ned, din Maane skal ej tage af; thi HERREN skal være dit Lys for evigt, dine Sørgedage har Ende.
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
Enhver i dit Folk er retfærdig, evigt ejer de Landet, et Skud, som HERREN har plantet, hans Hænders Værk, til hans Ære.
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”
Den mindste bliver en Stamme, den ringeste et talrigt Folk. Jeg er HERREN; naar Tid er inde, vil jeg fremme det i Hast.

< Ishaya 60 >