< Ishaya 6 >

1 A shekarar da Sarki Uzziya ya mutu, na ga Ubangiji zaune a kan kujerar sarauta a sama cike da ɗaukaka, zatinsa ya cika haikali.
In the year that King Uzziah died, I saw the Lord seated in majesty on a high throne, and the train of his robe filled the Temple.
2 A bisansa akwai serafofi, kowanne yana da fikafikai shida. Fikafikai biyu sun rufe fuskokinsu, da biyu suka rufe ƙafafunsu, biyu kuma da su suke tashi.
Seraphim stood above him, and each of them had six wings: They used two wings to cover their faces, two to cover their feet, and two to fly.
3 Suna kiran juna, “Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki! Ubangiji Maɗaukaki ne; duniya ta cika da ɗaukakarsa.”
They were calling out to one another: Holy, holy, holy is the Lord Almighty; his glory fills the whole earth.
4 Da jin ƙarar muryoyinsu madogarai da madogaran ƙofa suka girgiza, haikali kuma ya cika da hayaƙi.
The sound of their shouts made the doorposts and doorsteps shake, and the Temple was filled with smoke.
5 Sai na tā da murya na ce, “Kaitona! Na shiga uku! Gama ni mutum ne mai leɓuna marar tsarki, kuma ina raye a cikin mutane masu leɓuna marasa tsarki, idanuna kuma sun ga Sarki, Ubangiji Maɗaukaki.”
I cried out, “I'm doomed! I'm going to die because I'm a man of unclean lips, and I live among a people of unclean lips, for I've seen the King, the Lord Almighty!”
6 Sai ɗaya daga cikin serafofin ya yi firiya zuwa wurina tare da garwashi mai wuta a hannunsa, wanda ya ɗiba da arautaki daga bagade.
Then one of the seraphim flew over to me. He was holding a glowing coal that he had picked up with tongs from the altar.
7 Da shi ne ya taɓa bakina ya ce, “Duba, wannan ya taɓa leɓunanka, yanzu fa an kawar da laifofinka, an kuma gafarta maka zunubanka.”
He touched me on my mouth with it and told me, “Look! This has touched your lips, so now your guilt is taken away and your sin is forgiven.”
8 Sa’an nan na ji muryar Ubangiji tana cewa, “Wa zan aika? Wa zai tafi mana?” Sai na ce, “Ga ni! Ka aike ni!”
Then I heard the Lord asking, “Who shall I send? Who will go and speak for us?” So I said, “I'm here! Please send me!”
9 Ya ce, “Je ka ka faɗa wa wannan mutane, “‘Kome yawan kasa kunne da za ku yi, ba za ku fahimta ba; Kome yawan dubar da za ku yi, ba za ku san abin da yake faruwa ba.’
He replied, “Go and tell this people: ‘Keep on listening, but never understanding. Keep on seeing, but never comprehending.’
10 Ka sa zuciyar mutanen nan ta dushe; kunnuwansu su kurunce, idanunsu kuma su makance. In ba haka ba za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su fahimta da zuciyarsu, su kuma juyo a kuma warkar da su.”
Make the minds of this people insensitive; make their ears deaf and shut their eyes. Otherwise they might see with their eyes, hear with their ears, understand with their minds, and repent and be healed.”
11 Sa’an nan na ce, “Har yaushe, ya Ubangiji?” Ya kuma amsa, “Sai an lalatar da biranen ba kowa a ciki, sai an mai da gidaje kangwaye ƙasa kuma ta zama kango ba amfani,
Then I asked, “How long will this last, Lord?” He replied, “Until towns are ruined and empty, houses are abandoned, and the land is devastated and destroyed;
12 sai lokacin da Ubangiji ya kori kowa aka kuma yashe ƙasar gaba ɗaya.
until the Lord sends the people far away and the country is totally deserted.
13 Ko da yake kashi ɗaya bisa goma zai ragu a ƙasar, za tă sāke zama kango. Amma kamar yadda katambiri da itacen oak sukan bar kututturai sa’ad da aka yanke su, haka iri mai tsarkin nan zai zama kututture a ƙasar mai tsarki.”
Even though a tenth of the population remains in the land, it will be destroyed again. But in the same way as the terebinth and oak trees leave stumps when they're cut down, so the holy seed will remain as stump.”

< Ishaya 6 >