< Ishaya 6 >

1 A shekarar da Sarki Uzziya ya mutu, na ga Ubangiji zaune a kan kujerar sarauta a sama cike da ɗaukaka, zatinsa ya cika haikali.
Léta, kteréhož umřel král Uziáš, viděl jsem Pána sedícího na trůnu vysokém a vyzdviženém, a podolek jeho naplňoval chrám.
2 A bisansa akwai serafofi, kowanne yana da fikafikai shida. Fikafikai biyu sun rufe fuskokinsu, da biyu suka rufe ƙafafunsu, biyu kuma da su suke tashi.
Serafínové stáli nad ním. Šest křídel měl každý z nich: dvěma zakrýval tvář svou, a dvěma přikrýval nohy své, a dvěma létal.
3 Suna kiran juna, “Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki! Ubangiji Maɗaukaki ne; duniya ta cika da ɗaukakarsa.”
A volal jeden k druhému, říkaje: Svatý, svatý, svatý Hospodin zástupů, plná jest všecka země slávy jeho.
4 Da jin ƙarar muryoyinsu madogarai da madogaran ƙofa suka girgiza, haikali kuma ya cika da hayaƙi.
A pohnuly se podvoje veřejí od hlasu volajícího, a dům plný byl dymu.
5 Sai na tā da murya na ce, “Kaitona! Na shiga uku! Gama ni mutum ne mai leɓuna marar tsarki, kuma ina raye a cikin mutane masu leɓuna marasa tsarki, idanuna kuma sun ga Sarki, Ubangiji Maɗaukaki.”
I řekl jsem: Běda mně, jižť zahynu, proto že jsem člověk poškvrněné rty maje, k tomu u prostřed lidu rty poškvrněné majícího bydlím, a že krále Hospodina zástupů viděly oči mé.
6 Sai ɗaya daga cikin serafofin ya yi firiya zuwa wurina tare da garwashi mai wuta a hannunsa, wanda ya ɗiba da arautaki daga bagade.
I přiletěl ke mně jeden z serafínů, maje v ruce své uhel řeřavý, kleštěmi vzatý z oltáře,
7 Da shi ne ya taɓa bakina ya ce, “Duba, wannan ya taɓa leɓunanka, yanzu fa an kawar da laifofinka, an kuma gafarta maka zunubanka.”
A dotekl se úst mých, a řekl: Aj hle, dotekl se uhel tento úst tvých; nebo odešla nepravost tvá, a hřích tvůj shlazen jest.
8 Sa’an nan na ji muryar Ubangiji tana cewa, “Wa zan aika? Wa zai tafi mana?” Sai na ce, “Ga ni! Ka aike ni!”
Potom slyšel jsem hlas Pána řkoucího: Koho pošli? A kdo nám půjde? I řekl jsem: Aj já, pošli mne.
9 Ya ce, “Je ka ka faɗa wa wannan mutane, “‘Kome yawan kasa kunne da za ku yi, ba za ku fahimta ba; Kome yawan dubar da za ku yi, ba za ku san abin da yake faruwa ba.’
On pak řekl: Jdi, a rci lidu tomu: Slyšte slyšíce, a nerozumějte, a hleďte hledíce, a nepoznávejte.
10 Ka sa zuciyar mutanen nan ta dushe; kunnuwansu su kurunce, idanunsu kuma su makance. In ba haka ba za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su fahimta da zuciyarsu, su kuma juyo a kuma warkar da su.”
Zatvrď srdce lidu toho, a uši jeho zacpej, a oči jeho zavři, aby neviděl očima svýma, a ušima svýma neslyšel, a srdcem svým nerozuměl, a neobrátil se, a nebyl uzdraven.
11 Sa’an nan na ce, “Har yaushe, ya Ubangiji?” Ya kuma amsa, “Sai an lalatar da biranen ba kowa a ciki, sai an mai da gidaje kangwaye ƙasa kuma ta zama kango ba amfani,
A když jsem řekl: Až dokud, Pane? i odpověděl: Dokudž nezpustnou města, tak aby nebylo žádného obyvatele, a domové, aby nebylo v nich žádného člověka, a země docela nezpustne,
12 sai lokacin da Ubangiji ya kori kowa aka kuma yashe ƙasar gaba ɗaya.
A nevzdálí Hospodin všelikého člověka, a nebude dokonalého zpuštění u prostřed země;
13 Ko da yake kashi ɗaya bisa goma zai ragu a ƙasar, za tă sāke zama kango. Amma kamar yadda katambiri da itacen oak sukan bar kututturai sa’ad da aka yanke su, haka iri mai tsarkin nan zai zama kututture a ƙasar mai tsarki.”
Dokudž ještě v ní nebude desateré zhouby, a teprv zkažena bude. Ale jakož ono jilmoví, a jako doubí onoho náspu podporou jest, tak símě svaté jest podpora její.

< Ishaya 6 >