< Ishaya 59 >

1 Tabbatacce hannun Ubangiji bai kāsa yin ceto ba, kunnensa kuma bai kurmance da zai kāsa ji ba.
هان دست خداوند کوتاه نیست تانرهاند و گوش او سنگین نی تا نشنود.۱
2 Amma laifofinku sun raba ku da Allahnku; zunubanku sun ɓoye fuskarsa daga gare ku, saboda kada yă ji.
لیکن خطایای شما در میان شما و خدای شماحایل شده است و گناهان شما روی او را از شماپوشانیده است تا نشنود.۲
3 Gama hannuwanku sun ƙazantu da jini, yatsotsinku kuma da alhaki. Leɓunanku suna faɗin ƙarairayi, harshenku kuma yana raɗar mugayen abubuwa.
زیرا که دستهای شمابه خون و انگشتهای شما به شرارت آلوده شده است. لبهای شما به دروغ تکلم می‌نماید وزبانهای شما به شرارت تنطق می‌کند.۳
4 Babu wani mai ce a yi adalci; babu wani mai nema a dubi al’amarinsa da mutunci. Sun dogara a gardandamin banza suna ƙarairayi; suna ɗaukar cikin ɓarna, su haifi mugunta.
احدی به عدالت دعوی نمی کند و هیچکس به راستی داوری نمی نماید. به بطالت توکل دارند و به دروغ تکلم می‌نمایند. به ظلم حامله شده، شرارت رامی زایند.۴
5 Suna ƙyanƙyashe ƙwan kāsā su kuma saƙa yanar gizo-gizo. Duk wanda ya ci ƙwansu zai mutu, kuma sa’ad da ƙwan ya fashe, zai ƙyanƙyashe kububuwa.
از تخمهای افعی بچه برمی آورند وپرده عنکبوت می‌بافند. هرکه از تخمهای ایشان بخورد می‌میرد و آن چون شکسته گردد افعی بیرون می‌آید.۵
6 Yanar gizo-gizonsu ba amfani don tufa; ba za su iya rufuwa da abin da suka yi ba. Ayyukansu mugaye ne, ayyukan tā da hargitsi kuma suna a hannuwansu.
پرده های ایشان لباس نخواهدشد و خویشتن را از اعمال خود نخواهند پوشانیدزیرا که اعمال ایشان اعمال شرارت است و عمل ظلم در دستهای ایشان است.۶
7 Ƙafafunsu sukan gaggauta zuwa aikata zunubi; suna da saurin zub da jini. Tunaninsu mugaye ne; lalaci da hallaka sun shata hanyoyinsu.
پایهای ایشان برای بدی دوان و به جهت ریختن خون بی‌گناهان شتابان است. افکار ایشان افکار شرارت است ودر راههای ایشان ویرانی و خرابی است.۷
8 Ba su san hanyar salama ba; babu adalci a hanyoyinsu. Sun mai da su karkatattun hanyoyi; babu wanda zai yi tafiya a kansu ya sami salama.
طریق سلامتی را نمی دانند و در راههای ایشان انصاف نیست. جاده های کج برای خود ساخته‌اند و هر‌که در آنها سالک باشد سلامتی را نخواهد دانست.۸
9 Saboda haka gaskiya ta yi nisa da mu, adalci kuma ba ya kaiwa gare mu. Muna neman haske, sai ga duhu; muna neman haske, sai muka yi ta tafiya cikin baƙin inuwa.
بنابراین انصاف از ما دور شده است و عدالت به ما نمی رسد. انتظار نور می‌کشیم و اینک ظلمت است و منتظر روشنایی هستیم اما در تاریکی غلیظ سالک می‌باشیم.۹
10 Kamar makafi, sai lallubar bango muke yi, muna lallubawar hanyarmu kamar marasa idanu. Da tsakar rana muna tuntuɓe sai ka ce wuri ya fara duhu; cikin ƙarfafa, mun zama kamar matattu.
و مثل کوران برای دیوار تلمس می‌نماییم و مانند بی‌چشمان کورانه راه می‌رویم. در وقت ظهر مثل شام لغزش می‌خوریم و در میان تندرستان مانند مردگانیم.۱۰
11 Muna gurnani kamar beyar; muna ta ƙugi kamar kurciyoyi. Muna ta neman adalci amma ina; mun nemi fansa, amma yana can da nisa.
جمیع ما مثل خرسها صدا می‌کنیم و مانندفاخته‌ها ناله می‌نماییم، برای انصاف انتظارمی کشیم و نیست و برای نجات و از ما دورمی شود.۱۱
12 Gama laifofinmu suna da yawa a gabanka, zunubanmu kuma suna ba da shaida gāba da mu. Laifofinmu kullum suna a gabanmu, muna kuma sane da laifofinmu,
زیرا که خطایای ما به حضور تو بسیار شده و گناهان ما به ضد ما شهادت می‌دهد چونکه خطایای ما با ما است و گناهان خود را می‌دانیم.۱۲
13 tawaye da mūsun Ubangiji, mun juye bayanmu ga Allahnmu, zugawa a yi zalunci da tayarwa, faɗin ƙarairayi da zukatanmu suka shirya.
مرتد شده، خداوند را انکار نمودیم. از پیروی خدای خود انحراف ورزیدیم به ظلم و فتنه تکلم کردیم و به سخنان کذب حامله شده، از دل آنها راتنطق نمودیم.۱۳
14 Saboda haka aka kau da yin gaskiya adalci kuma ya tsaya can da nesa; gaskiya ta yi tuntuɓe a tituna, sahihanci ba zai shiga ba.
و انصاف به عقب رانده شده وعدالت از ما دور ایستاده است زیرا که راستی درکوچه‌ها افتاده است و استقامت نمی تواند داخل شود.۱۴
15 Gaskiya ta ɓace gaba ɗaya, kuma duk wanda ya guji mugunta zai zama ganima. Ubangiji ya duba bai kuwa ji daɗi cewa babu adalci ba.
و راستی مفقود شده است و هر‌که ازبدی اجتناب نماید خود را به یغما می‌سپارد. وچون خداوند این را دید در نظر او بد آمد که انصاف وجود نداشت.۱۵
16 Ya ga cewa babu wani, ya yi mamaki cewa babu wanda zai shiga tsakani; saboda haka hannunsa ya aikata masa ceto, adalcinsa kuma ya raya shi.
و او دید که کسی نبود وتعجب نمود که شفاعت کننده‌ای وجود نداشت از این جهت بازوی وی برای او نجات آورد وعدالت او وی را دستگیری نمود.۱۶
17 Ya yafa sulke a matsayin rigar ƙirji, da hulan kwanon ceto a kansa; ya sa rigunan ɗaukar fansa ya kuma nannaɗe kansa da kishi kamar a cikin alkyabba.
پس عدالت را مثل زره پوشید و خود نجات را بر سر خویش نهاد. و جامه انتقام را به‌جای لباس در بر کرد وغیرت را مثل ردا پوشید.۱۷
18 Bisa ga abin da suka yi, haka za a sāka fushi a kan abokan gābansa ramuwa kuma a kan maƙiyansa; zai sāka wa tsibirai abin da ya dace da su.
بر وفق اعمال ایشان، ایشان را جزا خواهد داد. به خصمان خود حدت خشم را و به دشمنان خویش مکافات و به جزایرپاداش را خواهد رسانید.۱۸
19 Daga yamma, mutane za su ji tsoron Ubangiji, daga mafitar rana kuma, za su girmama ɗaukakarsa. Gama zai zo kamar rigyawa mai tsananin gudu cewa numfashin Ubangiji zai tafi tare da shi.
و از طرف مغرب ازنام یهوه و از طلوع آفتاب از جلال وی خواهندترسید زیرا که او مثل نهر سرشاری که باد خداوندآن را براند خواهد آمد.۱۹
20 “Mai fansa zai zo Sihiyona, zuwa waɗanda suke cikin Yaƙub da suka tuba daga zunubansu,” in ji Ubangiji.
و خداوند می‌گوید که نجات‌دهنده‌ای برای صهیون و برای آنانی که دریعقوب از معصیت بازگشت نمایند خواهد آمد.۲۰
21 “Game da ni dai, ga alkawarina da su,” in ji Ubangiji. “Ruhuna, wanda yake a kanka, da kuma maganata da na sa a bakinka ba za tă rabu da bakinka ba, ko daga bakunan’ya’yanka ba, ko kuwa daga bakunan zuriyarsu ba daga wannan lokaci zuwa gaba da kuma har abada,” in ji Ubangiji.
و خداوند می‌گوید: «اما عهد من با ایشان این است که روح من که بر تو است و کلام من که دردهان تو گذاشته‌ام از دهان تو و از دهان ذریت تو واز دهان ذریت ذریت تو دور نخواهد شد.» خداوند می‌گوید: «از الان و تا ابدالاباد.»۲۱

< Ishaya 59 >