< Ishaya 59 >

1 Tabbatacce hannun Ubangiji bai kāsa yin ceto ba, kunnensa kuma bai kurmance da zai kāsa ji ba.
Lo! the hand of Yahweh is not too short to save, —Neither is his ear too heavy to hear.
2 Amma laifofinku sun raba ku da Allahnku; zunubanku sun ɓoye fuskarsa daga gare ku, saboda kada yă ji.
But, your iniquities, have become separators betwixt you and your God, And your sins, have caused a hiding of face from you that he should-not hear.
3 Gama hannuwanku sun ƙazantu da jini, yatsotsinku kuma da alhaki. Leɓunanku suna faɗin ƙarairayi, harshenku kuma yana raɗar mugayen abubuwa.
For, your hands, are defiled with blood, And, your fingers, with iniquity, —Your lips, have spoken falsehood, and Your tongue, muttereth, perversity.
4 Babu wani mai ce a yi adalci; babu wani mai nema a dubi al’amarinsa da mutunci. Sun dogara a gardandamin banza suna ƙarairayi; suna ɗaukar cikin ɓarna, su haifi mugunta.
None, sueth in righteousness, and None, pleadeth in faithfulness, —Men are trusting in confusion, And speaking vanity, Conceiving wickedness And bringing forth iniquity:
5 Suna ƙyanƙyashe ƙwan kāsā su kuma saƙa yanar gizo-gizo. Duk wanda ya ci ƙwansu zai mutu, kuma sa’ad da ƙwan ya fashe, zai ƙyanƙyashe kububuwa.
Viper’s eggs, do they hatch, Spider’s threads, do they weave, —He that eateth of their eggs, dieth, And, that which is crushed, bringeth forth an adder;
6 Yanar gizo-gizonsu ba amfani don tufa; ba za su iya rufuwa da abin da suka yi ba. Ayyukansu mugaye ne, ayyukan tā da hargitsi kuma suna a hannuwansu.
Their threads, shall not become a garment, Neither shall they cover themselves with their fabrics, —Their fabrics, are fabrics of iniquity, Yea the product of violence is in their hands;
7 Ƙafafunsu sukan gaggauta zuwa aikata zunubi; suna da saurin zub da jini. Tunaninsu mugaye ne; lalaci da hallaka sun shata hanyoyinsu.
Their feet, to mischief, do run, And they speed to shed innocent blood, —Their devices, are devices of iniquity, Wasting and destruction, are in their high roads;
8 Ba su san hanyar salama ba; babu adalci a hanyoyinsu. Sun mai da su karkatattun hanyoyi; babu wanda zai yi tafiya a kansu ya sami salama.
the way of well-being, have they not known, And there is no justice in their tracks, —Their paths, have they made crooked for themselves, None who treadeth therein knoweth well—being.
9 Saboda haka gaskiya ta yi nisa da mu, adalci kuma ba ya kaiwa gare mu. Muna neman haske, sai ga duhu; muna neman haske, sai muka yi ta tafiya cikin baƙin inuwa.
For this cause, hath justice removed far from us, And righteousness overtaketh us not, —We wait for light, But lo! darkness, For brightness, In thick darkness, we walk:
10 Kamar makafi, sai lallubar bango muke yi, muna lallubawar hanyarmu kamar marasa idanu. Da tsakar rana muna tuntuɓe sai ka ce wuri ya fara duhu; cikin ƙarfafa, mun zama kamar matattu.
We grope, as blind men for a wall, Yea, as men without eyes, do we grope, —We have stumbled at broad noon as though it were twilight, In desolate places like the dead!
11 Muna gurnani kamar beyar; muna ta ƙugi kamar kurciyoyi. Muna ta neman adalci amma ina; mun nemi fansa, amma yana can da nisa.
We growl like bears all of us, And, like doves, do we, mournfully coo, —We wait For justice, and there is none, For salvation it is far from us!
12 Gama laifofinmu suna da yawa a gabanka, zunubanmu kuma suna ba da shaida gāba da mu. Laifofinmu kullum suna a gabanmu, muna kuma sane da laifofinmu,
For our transgressions have multiplied before thee, And, our sins, have witnessed against us, —For, our transgressions, are with us, And as for our iniquities, we acknowledge them:
13 tawaye da mūsun Ubangiji, mun juye bayanmu ga Allahnmu, zugawa a yi zalunci da tayarwa, faɗin ƙarairayi da zukatanmu suka shirya.
Transgressing, and denying Yahweh, And turning away from following our God, —Speaking oppression and revolt, Conceiving, and muttering from the heart, words of falsehood.
14 Saboda haka aka kau da yin gaskiya adalci kuma ya tsaya can da nesa; gaskiya ta yi tuntuɓe a tituna, sahihanci ba zai shiga ba.
So then there hath been a driving back of justice, And righteousness, afar off, standeth, —For truth, hath stumbled in the broad-way, And, right, cannot enter;
15 Gaskiya ta ɓace gaba ɗaya, kuma duk wanda ya guji mugunta zai zama ganima. Ubangiji ya duba bai kuwa ji daɗi cewa babu adalci ba.
And the truth hath been found missing, And he that hath turned away from wrong is liable to be despoiled, And when, Yahweh, looked, Then was it grievous in his eyes that there was no justice:
16 Ya ga cewa babu wani, ya yi mamaki cewa babu wanda zai shiga tsakani; saboda haka hannunsa ya aikata masa ceto, adalcinsa kuma ya raya shi.
When he saw that there was no mighty man, Then was he astonished that there was none to interpose, —So his own arm brought him salvation, And his own righteousness, the same, upheld him;
17 Ya yafa sulke a matsayin rigar ƙirji, da hulan kwanon ceto a kansa; ya sa rigunan ɗaukar fansa ya kuma nannaɗe kansa da kishi kamar a cikin alkyabba.
And he put on Righteousness as a coat of mail, And a helmet of victory upon his head, —And he put on the garments of avenging, for clothing, And wrapped about him as a cloak—jealousy,
18 Bisa ga abin da suka yi, haka za a sāka fushi a kan abokan gābansa ramuwa kuma a kan maƙiyansa; zai sāka wa tsibirai abin da ya dace da su.
According to their deeds, accordingly, will he repay, Indignation to his adversaries, Recompense to his enemies, —To the Coastlands—recompense, will he repay:
19 Daga yamma, mutane za su ji tsoron Ubangiji, daga mafitar rana kuma, za su girmama ɗaukakarsa. Gama zai zo kamar rigyawa mai tsananin gudu cewa numfashin Ubangiji zai tafi tare da shi.
That they may revere—From the West the name of Yahweh, And from the Rising of the Sun his glory, For he will come in like a rushing stream, the breath of Yahweh, driving it on;
20 “Mai fansa zai zo Sihiyona, zuwa waɗanda suke cikin Yaƙub da suka tuba daga zunubansu,” in ji Ubangiji.
So shall come in for Zion, a Redeemer, Even for such as are turning from transgression in Jacob, —Declareth Yahweh.
21 “Game da ni dai, ga alkawarina da su,” in ji Ubangiji. “Ruhuna, wanda yake a kanka, da kuma maganata da na sa a bakinka ba za tă rabu da bakinka ba, ko daga bakunan’ya’yanka ba, ko kuwa daga bakunan zuriyarsu ba daga wannan lokaci zuwa gaba da kuma har abada,” in ji Ubangiji.
And as for me, this, shall be my covenant with them, Saith Yahweh: My spirit that is upon thee, And my words which I have put in thy mouth, —Shall not be taken out of thy mouth—Nor out of the mouth of thy seed. Nor out of the mouth of thy seeds seed, Saith Yahweh, From henceforth even unto times age-abiding.

< Ishaya 59 >