< Ishaya 59 >

1 Tabbatacce hannun Ubangiji bai kāsa yin ceto ba, kunnensa kuma bai kurmance da zai kāsa ji ba.
Behold, Jehovah's hand is not shortened, that it cannot save, nor his ear heavy, that it cannot hear.
2 Amma laifofinku sun raba ku da Allahnku; zunubanku sun ɓoye fuskarsa daga gare ku, saboda kada yă ji.
But your iniquities have separated between you and your God, and your sins have hid his face from you so that he will not hear.
3 Gama hannuwanku sun ƙazantu da jini, yatsotsinku kuma da alhaki. Leɓunanku suna faɗin ƙarairayi, harshenku kuma yana raɗar mugayen abubuwa.
For your hands are defiled with blood, and your fingers with iniquity. Your lips have spoken lies. Your tongue mutters wickedness.
4 Babu wani mai ce a yi adalci; babu wani mai nema a dubi al’amarinsa da mutunci. Sun dogara a gardandamin banza suna ƙarairayi; suna ɗaukar cikin ɓarna, su haifi mugunta.
No man sues in righteousness, and no man pleads in truth. They trust in vanity, and speak lies. They conceive mischief, and bring forth iniquity.
5 Suna ƙyanƙyashe ƙwan kāsā su kuma saƙa yanar gizo-gizo. Duk wanda ya ci ƙwansu zai mutu, kuma sa’ad da ƙwan ya fashe, zai ƙyanƙyashe kububuwa.
They hatch adders' eggs, and weave the spider's web. He who eats of their eggs dies, and that which is crushed breaks out into a viper.
6 Yanar gizo-gizonsu ba amfani don tufa; ba za su iya rufuwa da abin da suka yi ba. Ayyukansu mugaye ne, ayyukan tā da hargitsi kuma suna a hannuwansu.
Their webs shall not become garments, nor shall they cover themselves with their works. Their works are works of iniquity, and the act of violence is in their hands.
7 Ƙafafunsu sukan gaggauta zuwa aikata zunubi; suna da saurin zub da jini. Tunaninsu mugaye ne; lalaci da hallaka sun shata hanyoyinsu.
Their feet run to evil, and they make haste to shed innocent blood. Their thoughts are thoughts of iniquity. Desolation and destruction are in their paths.
8 Ba su san hanyar salama ba; babu adalci a hanyoyinsu. Sun mai da su karkatattun hanyoyi; babu wanda zai yi tafiya a kansu ya sami salama.
They do not know the way of peace, and there is no justice in their goings. They have made them crooked paths. Whoever goes in it does not know peace.
9 Saboda haka gaskiya ta yi nisa da mu, adalci kuma ba ya kaiwa gare mu. Muna neman haske, sai ga duhu; muna neman haske, sai muka yi ta tafiya cikin baƙin inuwa.
Therefore justice is far from us, nor does righteousness overtake us. We look for light, but behold, darkness, for brightness, but we walk in obscurity.
10 Kamar makafi, sai lallubar bango muke yi, muna lallubawar hanyarmu kamar marasa idanu. Da tsakar rana muna tuntuɓe sai ka ce wuri ya fara duhu; cikin ƙarfafa, mun zama kamar matattu.
We grope for the wall like the blind. Yea, we grope as those who have no eyes. We stumble at noonday as in the twilight. We are as dead men in desolate places.
11 Muna gurnani kamar beyar; muna ta ƙugi kamar kurciyoyi. Muna ta neman adalci amma ina; mun nemi fansa, amma yana can da nisa.
We all roar like bears, and moan greatly like doves. We look for justice, but there is none, for salvation, but it is far off from us.
12 Gama laifofinmu suna da yawa a gabanka, zunubanmu kuma suna ba da shaida gāba da mu. Laifofinmu kullum suna a gabanmu, muna kuma sane da laifofinmu,
For our transgressions are multiplied before thee, and our sins testify against us. For our transgressions are with us, and as for our iniquities, we know them:
13 tawaye da mūsun Ubangiji, mun juye bayanmu ga Allahnmu, zugawa a yi zalunci da tayarwa, faɗin ƙarairayi da zukatanmu suka shirya.
transgressing and denying Jehovah, and turning away from following our God, speaking oppression and revolt, conceiving and uttering from the heart words of falsehood.
14 Saboda haka aka kau da yin gaskiya adalci kuma ya tsaya can da nesa; gaskiya ta yi tuntuɓe a tituna, sahihanci ba zai shiga ba.
And justice is turned away backward, and righteousness stands afar off. For truth has fallen in the street, and uprightness cannot enter.
15 Gaskiya ta ɓace gaba ɗaya, kuma duk wanda ya guji mugunta zai zama ganima. Ubangiji ya duba bai kuwa ji daɗi cewa babu adalci ba.
Yea, truth is lacking, and he who departs from evil makes himself a prey. And Jehovah saw it, and it displeased him that there was no justice.
16 Ya ga cewa babu wani, ya yi mamaki cewa babu wanda zai shiga tsakani; saboda haka hannunsa ya aikata masa ceto, adalcinsa kuma ya raya shi.
And he saw that there was no man, and wondered that there was no intercessor. Therefore his own arm brought salvation to him. And his righteousness, it upheld him.
17 Ya yafa sulke a matsayin rigar ƙirji, da hulan kwanon ceto a kansa; ya sa rigunan ɗaukar fansa ya kuma nannaɗe kansa da kishi kamar a cikin alkyabba.
And he put on righteousness as a breastplate, and a helmet of salvation upon his head. And he put on garments of vengeance for clothing, and was clad with zeal as a mantle.
18 Bisa ga abin da suka yi, haka za a sāka fushi a kan abokan gābansa ramuwa kuma a kan maƙiyansa; zai sāka wa tsibirai abin da ya dace da su.
According to their deeds, accordingly he will repay, wrath to his adversaries, recompense to his enemies. He will repay recompense to the islands.
19 Daga yamma, mutane za su ji tsoron Ubangiji, daga mafitar rana kuma, za su girmama ɗaukakarsa. Gama zai zo kamar rigyawa mai tsananin gudu cewa numfashin Ubangiji zai tafi tare da shi.
So they shall fear the name of Jehovah from the west, and his glory from the rising of the sun. For he will come as a rushing stream, which the breath of Jehovah drives.
20 “Mai fansa zai zo Sihiyona, zuwa waɗanda suke cikin Yaƙub da suka tuba daga zunubansu,” in ji Ubangiji.
And he who redeems will come to Zion, and to those who turn from transgression in Jacob, says Jehovah.
21 “Game da ni dai, ga alkawarina da su,” in ji Ubangiji. “Ruhuna, wanda yake a kanka, da kuma maganata da na sa a bakinka ba za tă rabu da bakinka ba, ko daga bakunan’ya’yanka ba, ko kuwa daga bakunan zuriyarsu ba daga wannan lokaci zuwa gaba da kuma har abada,” in ji Ubangiji.
And as for me, this is my covenant with them, says Jehovah: My Spirit that is upon thee, and my words which I have put in thy mouth, shall not depart out of thy mouth, nor out of the mouth of thy seed, nor out of the mouth of thy seed's seed, says Jehovah, from henceforth and forever.

< Ishaya 59 >