< Ishaya 58 >

1 “Ku yi ihu da ƙarfi, ba ƙaƙƙautawa. Ku tā da muryarku kamar busar ƙaho. Ku furta wa mutanena tawayensu da kuma ga gidan Yaƙub zunubansu.
Memeza ngomphimbo, ungayekeli, uphakamise ilizwi lakho njengophondo, utshele abantu bami isiphambeko sabo, lendlu kaJakobe izono zabo.
2 Gama kowace rana suna nemana; suna marmarin sanin hanyoyina, sai ka ce al’ummar da take yin abin da yake daidai ba ta kuma yashe umarnan Allahnta ba. Sun nemi shawarwaran da suke daidai daga gare ni suna kuma marmari Allah ya zo kusa da su.
Kanti bayangidinga mina usuku ngosuku, bethokoza ukwazi indlela zami; njengesizwe esenza ukulunga, esingadelanga isimiso sikaNkulunkulu waso, babuza kimi izimiso zokulunga, bathokoza ekusondeleni kuNkulunkulu.
3 Suna cewa, ‘Don me muka yi azumi, ba ka kuma gani ba? Me ya sa muka ƙasƙantar da kanmu, ba ka kuma lura da wannan ba?’ “Duk da haka a ranar azuminku, kuna yi yadda kuka ga dama kuna kuma zaluntar dukan ma’aikata.
Besithi: Kungani sizile ukudla, wena-ke ungaboni? Kungani sihluphe umphefumulo wethu, wena-ke ungakwazi? Khangelani, ngosuku lokuzila kwenu ukudla, lithola intokozo, licindezele zonke izisebenzi zenu.
4 Azuminku yakan ƙare a faɗa da kuma hargitsi, kuna ta naushin juna da mugayen naushe-naushe. Ba za ku iya azumi kamar yadda kuke yi a yau ku zaci za a ji muryarku can sama.
Khangelani, lizila ukudla lisenzela ingxabano lokuphikisana, lokutshaya ngenqindi yenkohlakalo; lingazili ukudla njengalamuhla, ukwenza ilizwi lenu lizwakale phezulu.
5 Irin azumin da na zaɓa ke nan, rana guda kawai don mutum ya ƙasƙantar da kansa? Sunkuyar da kanku kamar iwa kawai kuna kuma kwance a tsummoki da toka? Abin da kuke kira azumi ke nan rana yardajje ga Ubangiji?
Kunjalo yini ukuzila ukudla engikukhethileyo? Lusuku lokuthi umuntu ahluphe umphefumulo wakhe yini? Ukuthi akhothamise ikhanda lakhe njengomhlanga, endlale phansi kwakhe isaka lomlotha? Lokhu ungakubiza yini ngokuthi yikuzila ukudla, losuku olwemukelekayo eNkosini?
6 “Irin azumin da na zaɓa shi ne, a kunce sarƙoƙin rashin adalci a kuma kunce igiyoyin karkiya, a’yantar da waɗanda ake zalunta a kuma kakkarye kowace karkiya?
Kayisikho lokhu yini ukuzila ukudla engikukhethileyo: Ukuthukulula izibopho zobubi, ukukhulula imichilo yejogwe, ukuyekela abacindezelweyo bahambe bekhululekile, lokuthi lephule lonke ijogwe?
7 Ba shi ne ku rarraba abincinku da mayunwata ku kuma tanada wa matalauta masu yawo mahalli, sa’ad da kuka ga wanda yake tsirara, ku yi masa sutura, kada kuma ku ba wa namanku da jininku baya?
Kayisikho yini ukwabela olambileyo isinkwa sakho, lokungenisa abayanga abayimihambuma endlini, lapho ubona onqunu umembese, lokuthi ungacatsheli inyama yakho?
8 Sa’an nan haskenku zai keto kamar ketowar alfijir, warkarwarku kuma zai bayyana nan da nan; sa’an nan adalcinku zai tafi a gabanku, ɗaukakar Ubangiji kuma zai tsare ku daga baya.
Khona ukukhanya kwakho kuzaqhamuka njengokusa, lokusila kwakho kuhlume masinyane; lokulunga kwakho kuhambe phambi kwakho; inkazimulo yeNkosi ibe ngumvikeli wakho ngasemuva.
9 Sa’an nan za ku yi kira, Ubangiji kuma zai amsa; za ku yi kuka don neman taimako, zai kuwa ce ga ni nan. “In kuka kawar da karkiyar zalunci, kuka daina nuna wa juna yatsa da kuma faɗar mugayen maganganu,
Khona uzabiza, iNkosi iphendule, uzakhala, ibisisithi: Khangela ngilapha. Uba ususa phakathi kwakho ijogwe, ukukhomba ngomunwe, lokukhuluma okubi,
10 in kuma kuka ɗauki lokaci kuka ƙosar da mayunwata kuka kuma biya bukatun waɗanda suke shan tsanani, sa’an nan ne haskenku zai haskaka cikin duhu darenku kuma zai zama kamar tsakar rana.
ukhuphele olambileyo umphefumulo wakho, usuthise umphefumulo ohluphekileyo, khona ukukhanya kwakho kuzaphuma emnyameni, lobumnyama bakho bube njengemini enkulu.
11 Ubangiji zai bishe ku kullum; zai biya muku bukatunku a ƙasa mai zafin rana ya kuma ƙarfafa ƙasusuwanku. Za ku zama kamar lambun da aka yi masa banruwa, kamar rafin da ruwansa ba ya ƙafewa.
Njalo iNkosi izakukhokhela njalonjalo, isuthise umphefumulo wakho engwaduleni, iqinise amathambo akho, ube njengesivande esithelelwayo, lanjengomthombo wamanzi, omanzi awo angapheliyo.
12 Mutanenku za su sāke gina kufai na da su kuma daga tsofaffin harsashai; za a ce da ku Masu Gyaran Katangar da ta Rushe, Masu Farfaɗo da Tituna da kuma Wuraren zama.
Labakho bazakwakha amanxiwa amadala; uzavusa izisekelo zezizukulwana ngezizukulwana; uzabizwa ngokuthi: UMvalisikhala, uMbuyiseli wemikhondo yokuhlala.
13 “In kun kiyaye ƙafafunku daga take Asabbaci da kuma daga aikata abin da kuka gan dama a ranata mai tsarki, in kuka kira Asabbaci ranar murna rana mai tsarki ta Ubangiji kuma mai bangirma, in kuka girmama ta ta wurin ƙin yin abin da kuka gan dama da kuma yin al’amuranku ko yin mugayen maganganu,
Uba uphendula unyawo lwakho lusuka kusabatha, ungenzi intokozo yakho ngosuku lwami olungcwele; ulibize isabatha ngokuthi yintokozo, olungcwele lweNkosi, oluhloniphekayo; njalo uluhlonipha, ungenzi indlela zakho, ungatholi intokozo yakho, loba ukhulume ilizwi lakho,
14 sa’an nan za ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, zan kuma sa ku a kan maɗaukaka ƙasashe ku kuma yi biki a gādon mahaifinku Yaƙub.” Ni Ubangiji ne na faɗa.
khona uzazithokozisa eNkosini, ngizakugadisa ezindaweni eziphakemeyo zomhlaba, ngizakwenza udle ilifa likaJakobe uyihlo; ngoba umlomo weNkosi ukhulumile.

< Ishaya 58 >