< Ishaya 58 >

1 “Ku yi ihu da ƙarfi, ba ƙaƙƙautawa. Ku tā da muryarku kamar busar ƙaho. Ku furta wa mutanena tawayensu da kuma ga gidan Yaƙub zunubansu.
Crie à plein gosier, ne t'épargne point, élève ta voix comme un cor, et déclare à mon peuple leur iniquité, et à la maison de Jacob leurs péchés.
2 Gama kowace rana suna nemana; suna marmarin sanin hanyoyina, sai ka ce al’ummar da take yin abin da yake daidai ba ta kuma yashe umarnan Allahnta ba. Sun nemi shawarwaran da suke daidai daga gare ni suna kuma marmari Allah ya zo kusa da su.
Car ils me cherchent chaque jour, et prennent plaisir à savoir mes voies, comme une nation qui aurait suivi la justice, et qui n'aurait point abandonné le jugement de son Dieu; ils s'informent auprès des jugements de justice, et prennent plaisir à approcher de Dieu; [et puis ils disent];
3 Suna cewa, ‘Don me muka yi azumi, ba ka kuma gani ba? Me ya sa muka ƙasƙantar da kanmu, ba ka kuma lura da wannan ba?’ “Duk da haka a ranar azuminku, kuna yi yadda kuka ga dama kuna kuma zaluntar dukan ma’aikata.
Pourquoi avons-nous jeûné, et tu n'y as point eu d'égard? pourquoi avons-nous affligé nos âmes, et tu ne t'en es point soucié? Voici, au jour de votre jeûne vous trouvez votre volonté, et vous exigez tout ce en quoi vous tourmentez les autres.
4 Azuminku yakan ƙare a faɗa da kuma hargitsi, kuna ta naushin juna da mugayen naushe-naushe. Ba za ku iya azumi kamar yadda kuke yi a yau ku zaci za a ji muryarku can sama.
Voici, vous jeûnez pour faire des procès et des querelles, et pour frapper du poing méchamment; vous ne jeûnez point comme ce jour [le requerrait] afin de faire que votre voix soit exaucée d'en haut.
5 Irin azumin da na zaɓa ke nan, rana guda kawai don mutum ya ƙasƙantar da kansa? Sunkuyar da kanku kamar iwa kawai kuna kuma kwance a tsummoki da toka? Abin da kuke kira azumi ke nan rana yardajje ga Ubangiji?
Est-ce là le jeûne que j'ai choisi, que l'homme afflige son âme un jour? [Est-ce] en courbant sa tête comme le jonc, et en étendant le sac et la cendre? appelleras-tu cela un jeûne, et un jour agréable à l'Eternel?
6 “Irin azumin da na zaɓa shi ne, a kunce sarƙoƙin rashin adalci a kuma kunce igiyoyin karkiya, a’yantar da waɗanda ake zalunta a kuma kakkarye kowace karkiya?
N'est-ce pas plutôt ici le jeûne que j'ai choisi, que tu dénoues les liens de la méchanceté; que tu délies les cordages du joug, que tu laisses aller libres ceux qui sont foulés; et que vous rompiez tout joug?
7 Ba shi ne ku rarraba abincinku da mayunwata ku kuma tanada wa matalauta masu yawo mahalli, sa’ad da kuka ga wanda yake tsirara, ku yi masa sutura, kada kuma ku ba wa namanku da jininku baya?
N'est-ce pas que tu partages ton pain à celui qui a faim? et que tu fasses venir en ta maison les affligés qui sont errants? quand tu vois un homme nu, que tu le couvres, et que tu ne te caches point arrière de ta chair?
8 Sa’an nan haskenku zai keto kamar ketowar alfijir, warkarwarku kuma zai bayyana nan da nan; sa’an nan adalcinku zai tafi a gabanku, ɗaukakar Ubangiji kuma zai tsare ku daga baya.
Alors ta lumière éclôra comme l'aube du jour, et ta guérison germera incontinent, ta justice ira devant toi, [et] la gloire de l'Eternel sera ton arrière-garde.
9 Sa’an nan za ku yi kira, Ubangiji kuma zai amsa; za ku yi kuka don neman taimako, zai kuwa ce ga ni nan. “In kuka kawar da karkiyar zalunci, kuka daina nuna wa juna yatsa da kuma faɗar mugayen maganganu,
Alors tu prieras, et l'Eternel t'exaucera; tu crieras, et il dira; me voici. Si tu ôtes du milieu de toi le joug, [et que tu cesses] de hausser le doigt, [et] de dire des outrages;
10 in kuma kuka ɗauki lokaci kuka ƙosar da mayunwata kuka kuma biya bukatun waɗanda suke shan tsanani, sa’an nan ne haskenku zai haskaka cikin duhu darenku kuma zai zama kamar tsakar rana.
Si tu ouvres ton cœur à celui qui a faim, et que tu rassasies l'âme affligée; et ta lumière naîtra dans les ténèbres, et les ténèbres seront comme le Midi.
11 Ubangiji zai bishe ku kullum; zai biya muku bukatunku a ƙasa mai zafin rana ya kuma ƙarfafa ƙasusuwanku. Za ku zama kamar lambun da aka yi masa banruwa, kamar rafin da ruwansa ba ya ƙafewa.
Et l'Eternel te conduira continuellement, il rassasiera ton âme dans les grandes sécheresses, il engraissera tes os, et tu seras comme un jardin arrosé, et comme une source dont les eaux ne défaillent point.
12 Mutanenku za su sāke gina kufai na da su kuma daga tsofaffin harsashai; za a ce da ku Masu Gyaran Katangar da ta Rushe, Masu Farfaɗo da Tituna da kuma Wuraren zama.
Et [des gens sortiront] de toi qui rebâtiront les lieux déserts depuis longtemps; tu rétabliras les fondements [ruinés] depuis plusieurs générations; et on t'appellera le Réparateur des brèches, et le redresseur des chemins; afin qu'on habite [au pays].
13 “In kun kiyaye ƙafafunku daga take Asabbaci da kuma daga aikata abin da kuka gan dama a ranata mai tsarki, in kuka kira Asabbaci ranar murna rana mai tsarki ta Ubangiji kuma mai bangirma, in kuka girmama ta ta wurin ƙin yin abin da kuka gan dama da kuma yin al’amuranku ko yin mugayen maganganu,
Si tu retires ton pied du Sabbat, [toi] qui fais ta volonté au jour de ma sainteté; et si tu appelles le Sabbat tes délices, et honorable ce qui est saint à l'Eternel, et que tu l'honores en ne suivant point tes voies, ne trouvant point ta volonté, et n'usant point [de beaucoup] de paroles;
14 sa’an nan za ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, zan kuma sa ku a kan maɗaukaka ƙasashe ku kuma yi biki a gādon mahaifinku Yaƙub.” Ni Ubangiji ne na faɗa.
Alors tu jouiras de délices en l'Eternel, et je te ferai passer [comme] à cheval par-dessus les lieux haut élevés de la terre, et je te donnerai à manger l'héritage de Jacob ton père; car la bouche de l'Eternel a parlé.

< Ishaya 58 >