< Ishaya 58 >
1 “Ku yi ihu da ƙarfi, ba ƙaƙƙautawa. Ku tā da muryarku kamar busar ƙaho. Ku furta wa mutanena tawayensu da kuma ga gidan Yaƙub zunubansu.
« Criez à haute voix! N'épargnez pas! Élevez votre voix comme une trompette! Déclarez à mon peuple sa désobéissance, et à la maison de Jacob leurs péchés.
2 Gama kowace rana suna nemana; suna marmarin sanin hanyoyina, sai ka ce al’ummar da take yin abin da yake daidai ba ta kuma yashe umarnan Allahnta ba. Sun nemi shawarwaran da suke daidai daga gare ni suna kuma marmari Allah ya zo kusa da su.
Mais ils me cherchent chaque jour, et se réjouissent de connaître mes voies. Comme une nation qui a fait le bien, et n'ont pas abandonné l'ordonnance de leur Dieu, ils me demandent des jugements justes. Ils se plaisent à s'approcher de Dieu.
3 Suna cewa, ‘Don me muka yi azumi, ba ka kuma gani ba? Me ya sa muka ƙasƙantar da kanmu, ba ka kuma lura da wannan ba?’ “Duk da haka a ranar azuminku, kuna yi yadda kuka ga dama kuna kuma zaluntar dukan ma’aikata.
Pourquoi avons-nous jeûné, disent-ils, et ne voyez-vous pas? Pourquoi avons-nous affligé notre âme, et vous ne vous en apercevez pas? ». « Voici qu'au jour de ton jeûne tu trouves du plaisir, et opprimez tous vos ouvriers.
4 Azuminku yakan ƙare a faɗa da kuma hargitsi, kuna ta naushin juna da mugayen naushe-naushe. Ba za ku iya azumi kamar yadda kuke yi a yau ku zaci za a ji muryarku can sama.
Voici, vous jeûnez pour des querelles et des disputes, et de frapper avec le poing de la méchanceté. Vous ne jeûnez pas aujourd'hui pour faire entendre votre voix en haut lieu.
5 Irin azumin da na zaɓa ke nan, rana guda kawai don mutum ya ƙasƙantar da kansa? Sunkuyar da kanku kamar iwa kawai kuna kuma kwance a tsummoki da toka? Abin da kuke kira azumi ke nan rana yardajje ga Ubangiji?
Est-ce le jeûne que j'ai choisi? Un jour où un homme doit humilier son âme? Est-ce de baisser sa tête comme un roseau, et de se couvrir de sacs et de cendres? Vous appelez ça un jeûne, et un jour agréable pour Yahvé?
6 “Irin azumin da na zaɓa shi ne, a kunce sarƙoƙin rashin adalci a kuma kunce igiyoyin karkiya, a’yantar da waɗanda ake zalunta a kuma kakkarye kowace karkiya?
« N'est-ce pas là le jeûne que j'ai choisi: pour libérer les liens de la méchanceté, pour défaire les sangles de l'étrier, pour laisser les opprimés libres, et que vous brisez tout joug?
7 Ba shi ne ku rarraba abincinku da mayunwata ku kuma tanada wa matalauta masu yawo mahalli, sa’ad da kuka ga wanda yake tsirara, ku yi masa sutura, kada kuma ku ba wa namanku da jininku baya?
N'est-ce pas distribuer son pain à celui qui a faim, et que tu amènes les pauvres qui sont chassés dans ta maison? Quand tu vois le nu, que tu le couvres; et que tu ne te caches pas de ta propre chair?
8 Sa’an nan haskenku zai keto kamar ketowar alfijir, warkarwarku kuma zai bayyana nan da nan; sa’an nan adalcinku zai tafi a gabanku, ɗaukakar Ubangiji kuma zai tsare ku daga baya.
Alors ta lumière éclatera comme l'aurore, et votre guérison apparaîtra rapidement; alors ta justice marchera devant toi, et la gloire de Yahvé sera votre arrière-garde.
9 Sa’an nan za ku yi kira, Ubangiji kuma zai amsa; za ku yi kuka don neman taimako, zai kuwa ce ga ni nan. “In kuka kawar da karkiyar zalunci, kuka daina nuna wa juna yatsa da kuma faɗar mugayen maganganu,
Alors tu appelleras, et Yahvé répondra. Tu crieras à l'aide, et il dira: « Je suis là. « Si vous enlevez du milieu de vous le joug, le fait de pointer du doigt, et de parler méchamment;
10 in kuma kuka ɗauki lokaci kuka ƙosar da mayunwata kuka kuma biya bukatun waɗanda suke shan tsanani, sa’an nan ne haskenku zai haskaka cikin duhu darenku kuma zai zama kamar tsakar rana.
et si vous répandez votre âme à ceux qui ont faim, et satisfaire l'âme affligée, alors ta lumière se lèvera dans les ténèbres, et ton obscurité sera comme le jour de midi;
11 Ubangiji zai bishe ku kullum; zai biya muku bukatunku a ƙasa mai zafin rana ya kuma ƙarfafa ƙasusuwanku. Za ku zama kamar lambun da aka yi masa banruwa, kamar rafin da ruwansa ba ya ƙafewa.
et Yahvé te guidera sans cesse, satisfaire votre âme dans les lieux arides, et rendre vos os forts. Vous serez comme un jardin arrosé, et comme une source d'eau dont les eaux ne faiblissent pas.
12 Mutanenku za su sāke gina kufai na da su kuma daga tsofaffin harsashai; za a ce da ku Masu Gyaran Katangar da ta Rushe, Masu Farfaɗo da Tituna da kuma Wuraren zama.
Ceux qui seront de vous rebâtiront les anciennes ruines. Tu relèveras les fondations de nombreuses générations. Tu seras appelé Réparateur de la Brèche, Restaurateur de chemins avec des habitations.
13 “In kun kiyaye ƙafafunku daga take Asabbaci da kuma daga aikata abin da kuka gan dama a ranata mai tsarki, in kuka kira Asabbaci ranar murna rana mai tsarki ta Ubangiji kuma mai bangirma, in kuka girmama ta ta wurin ƙin yin abin da kuka gan dama da kuma yin al’amuranku ko yin mugayen maganganu,
« Si tu détournes ton pied du sabbat, de faire ton plaisir le jour de ma fête, et appeler le sabbat un délice, et le saint de Yahvé, honorable, et l'honorer, de ne pas faire à ta façon, ni de trouver son propre plaisir, ni de parler avec vos propres mots,
14 sa’an nan za ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, zan kuma sa ku a kan maɗaukaka ƙasashe ku kuma yi biki a gādon mahaifinku Yaƙub.” Ni Ubangiji ne na faɗa.
alors tu feras tes délices de Yahvé, et je vous ferai monter sur les hauteurs de la terre, et je te nourrirai de l'héritage de Jacob, ton père ». car la bouche de Yahvé l'a dit.