< Ishaya 58 >
1 “Ku yi ihu da ƙarfi, ba ƙaƙƙautawa. Ku tā da muryarku kamar busar ƙaho. Ku furta wa mutanena tawayensu da kuma ga gidan Yaƙub zunubansu.
Crye thou, ceesse thou not; as a trumpe enhaunse thi vois, and schewe thou to my puple her grete trespassis, and to the hous of Jacob her synnes.
2 Gama kowace rana suna nemana; suna marmarin sanin hanyoyina, sai ka ce al’ummar da take yin abin da yake daidai ba ta kuma yashe umarnan Allahnta ba. Sun nemi shawarwaran da suke daidai daga gare ni suna kuma marmari Allah ya zo kusa da su.
For thei seken me fro dai in to dai, and thei wolen knowe my weies; as a folk, that hath do riytfulnesse, and that hath not forsake the doom of her God; thei preien me domes of riytfulnesse, and wolen neiy to God.
3 Suna cewa, ‘Don me muka yi azumi, ba ka kuma gani ba? Me ya sa muka ƙasƙantar da kanmu, ba ka kuma lura da wannan ba?’ “Duk da haka a ranar azuminku, kuna yi yadda kuka ga dama kuna kuma zaluntar dukan ma’aikata.
Whi fastiden we, and thou biheldist not; we mekiden oure soulis, and thou knewist not? Lo! youre wille is foundun in the dai of youre fastyng, and ye axen alle youre dettouris.
4 Azuminku yakan ƙare a faɗa da kuma hargitsi, kuna ta naushin juna da mugayen naushe-naushe. Ba za ku iya azumi kamar yadda kuke yi a yau ku zaci za a ji muryarku can sama.
Lo! ye fasten to chidyngis and stryuyngis, and smyten with the fist wickidli. Nyl ye fast, as `til to this dai, that youre cry be herd an hiy.
5 Irin azumin da na zaɓa ke nan, rana guda kawai don mutum ya ƙasƙantar da kansa? Sunkuyar da kanku kamar iwa kawai kuna kuma kwance a tsummoki da toka? Abin da kuke kira azumi ke nan rana yardajje ga Ubangiji?
Whether sich is the fastyng which Y chees, a man to turmente his soule bi dai? whether to bynde his heed as a sercle, and to make redi a sak and aische? Whethir thou schalt clepe this a fastyng, and a dai acceptable to the Lord?
6 “Irin azumin da na zaɓa shi ne, a kunce sarƙoƙin rashin adalci a kuma kunce igiyoyin karkiya, a’yantar da waɗanda ake zalunta a kuma kakkarye kowace karkiya?
Whether not this is more the fastyng, which Y chees? Vnbynde thou the byndingis togidere of vnpitee, releesse thou birthuns pressynge doun; delyuere thou hem free, that ben brokun, and breke thou ech birthun.
7 Ba shi ne ku rarraba abincinku da mayunwata ku kuma tanada wa matalauta masu yawo mahalli, sa’ad da kuka ga wanda yake tsirara, ku yi masa sutura, kada kuma ku ba wa namanku da jininku baya?
Breke thi breed to an hungri man, and brynge in to thin hous nedi men and herborles; whanne thou seest a nakid man, hile thou hym, and dispise not thi fleisch.
8 Sa’an nan haskenku zai keto kamar ketowar alfijir, warkarwarku kuma zai bayyana nan da nan; sa’an nan adalcinku zai tafi a gabanku, ɗaukakar Ubangiji kuma zai tsare ku daga baya.
Thanne thi liyt schal breke out as the morewtid, and thin helthe schal rise ful soone; and thi riytfulnesse schal go bifore thi face, and the glorie of the Lord schal gadere thee.
9 Sa’an nan za ku yi kira, Ubangiji kuma zai amsa; za ku yi kuka don neman taimako, zai kuwa ce ga ni nan. “In kuka kawar da karkiyar zalunci, kuka daina nuna wa juna yatsa da kuma faɗar mugayen maganganu,
Thanne thou schalt clepe to help, and the Lord schal here; thou schalt crie, and he schal seie, Lo! Y am present, for Y am merciful, thi Lord God. If thou takist awei a chayne fro the myddis of thee, and ceessist to holde forth the fyngur, and to speke that profitith not;
10 in kuma kuka ɗauki lokaci kuka ƙosar da mayunwata kuka kuma biya bukatun waɗanda suke shan tsanani, sa’an nan ne haskenku zai haskaka cikin duhu darenku kuma zai zama kamar tsakar rana.
whanne thou schedist out thi soule to an hungri man, and fillist a soule, `that is turmentid, thi liyt schal rise in derknessis, and thi derknessis schulen be as myddai.
11 Ubangiji zai bishe ku kullum; zai biya muku bukatunku a ƙasa mai zafin rana ya kuma ƙarfafa ƙasusuwanku. Za ku zama kamar lambun da aka yi masa banruwa, kamar rafin da ruwansa ba ya ƙafewa.
And the Lord thi God schal yyue euere reste to thee, and schal fille thi soule with schynyngis, and schal delyuere thi boonys; and thou schalt be as a watri gardyn, and as a welle of watris, whose waters schulen not faile.
12 Mutanenku za su sāke gina kufai na da su kuma daga tsofaffin harsashai; za a ce da ku Masu Gyaran Katangar da ta Rushe, Masu Farfaɗo da Tituna da kuma Wuraren zama.
And the forsakun thingis of worldis schulen be bildid in thee, and thou schalt reise the foundementis of generacioun and generacioun; and thou schalt be clepid a bildere of heggis, turnynge awei the pathis of wickidnessis.
13 “In kun kiyaye ƙafafunku daga take Asabbaci da kuma daga aikata abin da kuka gan dama a ranata mai tsarki, in kuka kira Asabbaci ranar murna rana mai tsarki ta Ubangiji kuma mai bangirma, in kuka girmama ta ta wurin ƙin yin abin da kuka gan dama da kuma yin al’amuranku ko yin mugayen maganganu,
If thou turnest awei thi foot fro the sabat, to do thi wille in myn hooli dai, and clepist the sabat delicat, and hooli, the gloriouse of the Lord, and glorifiest him, while thou doist not thi weies, and thi wille is not foundun, that thou speke a word;
14 sa’an nan za ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, zan kuma sa ku a kan maɗaukaka ƙasashe ku kuma yi biki a gādon mahaifinku Yaƙub.” Ni Ubangiji ne na faɗa.
thanne thou schalt delite on the Lord, and Y schal reise thee on the hiynesse of erthe, and Y schal fede thee with the eritage of Jacob, thi fadir; for whi the mouth of the Lord spak.