< Ishaya 58 >

1 “Ku yi ihu da ƙarfi, ba ƙaƙƙautawa. Ku tā da muryarku kamar busar ƙaho. Ku furta wa mutanena tawayensu da kuma ga gidan Yaƙub zunubansu.
[Yahweh said to me], “Shout loudly! Shout like [SIM] a loud trumpet! Shout to warn my Israeli people about their sins [DOU]!
2 Gama kowace rana suna nemana; suna marmarin sanin hanyoyina, sai ka ce al’ummar da take yin abin da yake daidai ba ta kuma yashe umarnan Allahnta ba. Sun nemi shawarwaran da suke daidai daga gare ni suna kuma marmari Allah ya zo kusa da su.
They worship me every day; [they come to my temple because they say that] they are eager to know what I want them to do. They act as though they are a nation that does things that are righteous, who would never abandon their God. They request me to decide matters justly, and they delight to come to worship me.
3 Suna cewa, ‘Don me muka yi azumi, ba ka kuma gani ba? Me ya sa muka ƙasƙantar da kanmu, ba ka kuma lura da wannan ba?’ “Duk da haka a ranar azuminku, kuna yi yadda kuka ga dama kuna kuma zaluntar dukan ma’aikata.
[They say], ‘We have (fasted/abstained from eating food) to please you, but you did not [RHQ] notice our doing that. We humbled ourselves, but you did not [RHQ] pay any attention!’ I will tell you why I did not pay attention. It is because when you fast, you do it only to please yourselves, and you act cruelly toward all your workers.
4 Azuminku yakan ƙare a faɗa da kuma hargitsi, kuna ta naushin juna da mugayen naushe-naushe. Ba za ku iya azumi kamar yadda kuke yi a yau ku zaci za a ji muryarku can sama.
You fast, but you also quarrel and fight [with each other] with your fists. [Doing things like that while] you fast will [certainly] not cause [me] to hear your prayers [where I am], high in heaven.
5 Irin azumin da na zaɓa ke nan, rana guda kawai don mutum ya ƙasƙantar da kansa? Sunkuyar da kanku kamar iwa kawai kuna kuma kwance a tsummoki da toka? Abin da kuke kira azumi ke nan rana yardajje ga Ubangiji?
You [act as though] [IRO] you humble yourselves [RHQ] by bowing your heads like [SIM] [the tops of] reeds bend [when the wind blows], and you wear [RHQ] rough clothes and cover your heads with ashes [like people do when they are grieving]. That is what you do when you are fasting, but do you really think [RHQ] that will please me?
6 “Irin azumin da na zaɓa shi ne, a kunce sarƙoƙin rashin adalci a kuma kunce igiyoyin karkiya, a’yantar da waɗanda ake zalunta a kuma kakkarye kowace karkiya?
No, that is not the kind of fasting that I desire. What I really want [RHQ] is for you to free those who have been unjustly put in prison [DOU], and to encourage those who are (treated cruelly/oppressed); I want you to free those who have been oppressed in any way.
7 Ba shi ne ku rarraba abincinku da mayunwata ku kuma tanada wa matalauta masu yawo mahalli, sa’ad da kuka ga wanda yake tsirara, ku yi masa sutura, kada kuma ku ba wa namanku da jininku baya?
I want you to [RHQ] share your food with those who are hungry and to allow those who have no houses to stay in your houses. Give clothes to those who do not have clothes, and do not hide from your relatives who need help from you.
8 Sa’an nan haskenku zai keto kamar ketowar alfijir, warkarwarku kuma zai bayyana nan da nan; sa’an nan adalcinku zai tafi a gabanku, ɗaukakar Ubangiji kuma zai tsare ku daga baya.
If you do those things, [what you do for others will be like] [SIM] a light that shines when it dawns. The troubles [that have been caused by your sins] will end quickly. Others will know about your righteous behavior, and with my glorious presence I will protect you from behind [like I protected the Israeli people when they left Egypt].
9 Sa’an nan za ku yi kira, Ubangiji kuma zai amsa; za ku yi kuka don neman taimako, zai kuwa ce ga ni nan. “In kuka kawar da karkiyar zalunci, kuka daina nuna wa juna yatsa da kuma faɗar mugayen maganganu,
Then you will call out to me, and I will [quickly] answer [and say that I will help you].’ Stop (oppressing people/treating people cruelly); stop falsely accusing people; and stop saying evil [things about people].
10 in kuma kuka ɗauki lokaci kuka ƙosar da mayunwata kuka kuma biya bukatun waɗanda suke shan tsanani, sa’an nan ne haskenku zai haskaka cikin duhu darenku kuma zai zama kamar tsakar rana.
Give food to those who are hungry, and give to people who are afflicted/suffering the things that they need. [Your doing that will be like] [MET] a light that shines in the darkness; instead of doing evil to people [MET], [the good things that you do for them will be like] [SIM] sunshine at noontime.
11 Ubangiji zai bishe ku kullum; zai biya muku bukatunku a ƙasa mai zafin rana ya kuma ƙarfafa ƙasusuwanku. Za ku zama kamar lambun da aka yi masa banruwa, kamar rafin da ruwansa ba ya ƙafewa.
[I], Yahweh, will guide you continually, and I will give you good things to satisfy you. I will enable you to remain strong and healthy. You will be like [SIM] a garden that is well watered, like [SIM] a spring that never dries up.
12 Mutanenku za su sāke gina kufai na da su kuma daga tsofaffin harsashai; za a ce da ku Masu Gyaran Katangar da ta Rushe, Masu Farfaɗo da Tituna da kuma Wuraren zama.
[Your people] will rebuild the cities that were destroyed long ago; they will build [houses] on top of the old foundations. People will say that you are the ones who are repairing the holes [in the city walls], and who are repairing the streets where people live.
13 “In kun kiyaye ƙafafunku daga take Asabbaci da kuma daga aikata abin da kuka gan dama a ranata mai tsarki, in kuka kira Asabbaci ranar murna rana mai tsarki ta Ubangiji kuma mai bangirma, in kuka girmama ta ta wurin ƙin yin abin da kuka gan dama da kuma yin al’amuranku ko yin mugayen maganganu,
Do not travel [MTY] long distances on Sabbath/rest days, and on Sabbath days do not do only the things that you delight to do. Enjoy the Sabbath days, and consider them to be delightful. The Sabbath days are my holy days. Honor me, Yahweh, in everything that you do [on the Sabbath days]. Do not talk about and do things [only] to please yourselves. If you do all the things that I have just now told you to do,
14 sa’an nan za ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, zan kuma sa ku a kan maɗaukaka ƙasashe ku kuma yi biki a gādon mahaifinku Yaƙub.” Ni Ubangiji ne na faɗa.
I will enable you to be joyful. I will greatly honor you; [I will honor you everywhere!] I will give to you the [blessings] that I gave to your ancestor Jacob. [Those things will surely happen because I], Yahweh, have said it.”

< Ishaya 58 >