< Ishaya 58 >
1 “Ku yi ihu da ƙarfi, ba ƙaƙƙautawa. Ku tā da muryarku kamar busar ƙaho. Ku furta wa mutanena tawayensu da kuma ga gidan Yaƙub zunubansu.
Cry aloud, spare not. Lift up thy voice like a trumpet, and declare to my people their transgression, and to the house of Jacob their sins.
2 Gama kowace rana suna nemana; suna marmarin sanin hanyoyina, sai ka ce al’ummar da take yin abin da yake daidai ba ta kuma yashe umarnan Allahnta ba. Sun nemi shawarwaran da suke daidai daga gare ni suna kuma marmari Allah ya zo kusa da su.
Yet they seek me daily, and delight to know my ways. As a nation that did righteousness, and forsook not the ordinance of their God, they ask of me righteous judgments; they delight to draw near to God.
3 Suna cewa, ‘Don me muka yi azumi, ba ka kuma gani ba? Me ya sa muka ƙasƙantar da kanmu, ba ka kuma lura da wannan ba?’ “Duk da haka a ranar azuminku, kuna yi yadda kuka ga dama kuna kuma zaluntar dukan ma’aikata.
Why have we fasted, they say, and thou see not? We have afflicted our soul, and thou take no knowledge. Behold, in the day of your fast ye find pleasure, and exact from all your laborers.
4 Azuminku yakan ƙare a faɗa da kuma hargitsi, kuna ta naushin juna da mugayen naushe-naushe. Ba za ku iya azumi kamar yadda kuke yi a yau ku zaci za a ji muryarku can sama.
Behold, ye fast for strife and contention, and to smite with the fist of wickedness. Ye do not fast this day so as to make your voice to be heard on high.
5 Irin azumin da na zaɓa ke nan, rana guda kawai don mutum ya ƙasƙantar da kansa? Sunkuyar da kanku kamar iwa kawai kuna kuma kwance a tsummoki da toka? Abin da kuke kira azumi ke nan rana yardajje ga Ubangiji?
Is such the fast that I have chosen, the day for a man to afflict his soul? Is it to bow down his head as a rush, and to spread sackcloth and ashes under him? Will thou call this a fast, and an acceptable day to Jehovah?
6 “Irin azumin da na zaɓa shi ne, a kunce sarƙoƙin rashin adalci a kuma kunce igiyoyin karkiya, a’yantar da waɗanda ake zalunta a kuma kakkarye kowace karkiya?
Is not this the fast that I have chosen: to loose the bonds of wickedness, to undo the bands of the yoke, and to let the oppressed go free, and that ye break every yoke?
7 Ba shi ne ku rarraba abincinku da mayunwata ku kuma tanada wa matalauta masu yawo mahalli, sa’ad da kuka ga wanda yake tsirara, ku yi masa sutura, kada kuma ku ba wa namanku da jininku baya?
Is it not to deal thy bread to a hungry man, and that thou bring the poor who are cast out to thy house, when thou see a naked man, that thou cover him, and that thou not hide thyself from thine own flesh?
8 Sa’an nan haskenku zai keto kamar ketowar alfijir, warkarwarku kuma zai bayyana nan da nan; sa’an nan adalcinku zai tafi a gabanku, ɗaukakar Ubangiji kuma zai tsare ku daga baya.
Then thy light shall break forth as the morning, and thy healing shall spring forth speedily. And thy righteousness shall go before thee. The glory of Jehovah shall be thy rearward.
9 Sa’an nan za ku yi kira, Ubangiji kuma zai amsa; za ku yi kuka don neman taimako, zai kuwa ce ga ni nan. “In kuka kawar da karkiyar zalunci, kuka daina nuna wa juna yatsa da kuma faɗar mugayen maganganu,
Then thou shall call, and Jehovah will answer, thou shall cry, and he will say, Here I am. If thou take the yoke away from the midst of thee, the putting forth of the finger, and speaking wickedly,
10 in kuma kuka ɗauki lokaci kuka ƙosar da mayunwata kuka kuma biya bukatun waɗanda suke shan tsanani, sa’an nan ne haskenku zai haskaka cikin duhu darenku kuma zai zama kamar tsakar rana.
and if thou draw out thy soul to a hungry man, and satisfy an afflicted soul, then thy light shall rise in darkness, and thine obscurity be as the noonday.
11 Ubangiji zai bishe ku kullum; zai biya muku bukatunku a ƙasa mai zafin rana ya kuma ƙarfafa ƙasusuwanku. Za ku zama kamar lambun da aka yi masa banruwa, kamar rafin da ruwansa ba ya ƙafewa.
And Jehovah will guide thee continually, and satisfy thy soul in dry places, and make strong thy bones. And thou shall be like a watered garden, and like a spring of water whose waters fail not.
12 Mutanenku za su sāke gina kufai na da su kuma daga tsofaffin harsashai; za a ce da ku Masu Gyaran Katangar da ta Rushe, Masu Farfaɗo da Tituna da kuma Wuraren zama.
And those who shall be of thee shall build the old waste places. Thou shall raise up the foundations of many generations, and thou shall be called The repairer of the breach, The restorer of paths to dwell in.
13 “In kun kiyaye ƙafafunku daga take Asabbaci da kuma daga aikata abin da kuka gan dama a ranata mai tsarki, in kuka kira Asabbaci ranar murna rana mai tsarki ta Ubangiji kuma mai bangirma, in kuka girmama ta ta wurin ƙin yin abin da kuka gan dama da kuma yin al’amuranku ko yin mugayen maganganu,
If thou turn away thy foot from the sabbath, from doing thy pleasure on my holy day, and call the sabbath a delight, and the holy of Jehovah honorable, and shall honor it, not doing thine own ways, nor finding thine own pleasure, nor speaking thine own words:
14 sa’an nan za ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, zan kuma sa ku a kan maɗaukaka ƙasashe ku kuma yi biki a gādon mahaifinku Yaƙub.” Ni Ubangiji ne na faɗa.
then thou shall delight thyself in Jehovah, and I will make thee to ride upon the high places of the earth, and I will feed thee with the heritage of Jacob thy father. For the mouth of Jehovah has spoken it.