< Ishaya 57 >
1 Mai adalci yakan mutu, ba kuwa wanda yakan yi tunani a zuciyarsa; an kwashe mutanen kirki, ba kuwa wanda ya fahimta cewa an kwashe masu adalci don a tsame su daga mugunta.
Le juste est mort, et il n'y a personne qui y prenne garde; et les gens de bien sont recueillis, sans qu'on y soit attentif, [sans qu'on considère] que le juste a été recueilli de devant le mal.
2 Waɗanda suke aikata abin da yake daidai sukan shiga da salama; sukan huta yayinda suka kwanta cikin kabari.
Il entrera en paix, ils se reposent dans leurs sépulcres, [savoir] quiconque aura marché devant lui.
3 “Amma ku, ku matso nan, ku’ya’ya maza na masu sihiri, ku zuriyar mazinata da karuwai!
Mais vous enfants de la devineresse, race adultère, et qui paillardez, approchez ici.
4 Wane ne kuke yi wa ba’a? Ga wa kuke masa gwalo kuna kuma fitar da harshe? Ashe, ku ba tarin’yan tawaye ba ne, zuriyar maƙaryata?
De qui vous êtes-vous moqués? contre qui avez-vous ouvert la bouche, [et] tiré la langue? n'êtes-vous pas des enfants prévaricateurs, et une fausse race?
5 Kuna cike da muguwar sha’awa mai ƙonawa a cikin itatuwan oak da kuma a ƙarƙashin kowane itace mai inuwa; kuna miƙa hadayar’ya’yanku a rafuffuka da kuma a ƙarƙashin tsagaggun duwatsu.
Qui vous échauffez après les chênes, [et] sous tout arbre vert; et qui égorgez les enfants dans les vallées, sous les quartiers des rochers.
6 Gumakan da suke cikin duwatsu masu sulɓi su ne rabonku; su ɗin, su ne rabonku. I, gare su kuka kwarara hadayu na sha kuka kuma miƙa hadayu na gari. Saboda waɗannan abubuwa, zan yi haƙuri?
Ta portion est dans les pierres polies des torrents; ce sont elles, ce sont elles, qui sont ton lot; tu leur as aussi répandu ton aspersion, tu leur as offert des offrandes; pourrai-je être content de ces choses?
7 Kun yi gadonku a dogayen duwatsu masu tsayi da kuma a tudu mai tsawo; a can kuka haura don ku miƙa hadayunku.
Tu as mis ton lit sur les montagnes hautes et élevées, même tu y es montée pour faire des sacrifices.
8 A bayan ƙofofi da madogaran ƙofofi kuka kafa alamun gumakanku. Kuka yashe ni, kuka kware gadonku, kuka kwanta a kansa kuka fadada shi; kuka kuma ƙulla yarjejjeniya da waɗanda kuke ƙaunar gadajensu, kuka dubi tsiraicinsu.
Et tu as mis derrière la porte et [derrière] le poteau ton mémorial, car tu t'es découverte loin de moi, et tu es montée, tu as élargi ton lit, et tu te l'es taillé [plus grand] que n'ont fait ceux-là; tu as aimé leur lit, tu as pris garde aux belles places.
9 Kuka tafi wurin Molek da man zaitun kuka kuma riɓaɓɓanya turarenku. Kuka aika jakadunku can da nisa; kuka gangara zuwa cikin kabari kansa! (Sheol )
Tu as voyagé vers le Roi avec des onguents précieux, et tu as ajouté parfums sur parfums; tu as envoyé tes ambassades bien loin, et tu t'es abaissée jusqu'aux enfers. (Sheol )
10 Kuka gaji cikin dukan al’amuranku, amma ba ku iya cewa, ‘Aikin banza ne ba.’ Kuka sami sabuntar ƙarfinku, ta haka ba ku suma ba.
Tu t'es travaillée dans la longueur de ton chemin, et tu n'as point dit; c'en est fait. Tu as trouvé la vigueur de ta main, et à cause de cela tu n'as point été languissante.
11 “Wa ya sa ku fargaba, kuna jin tsoro har kuka yi mini ƙarya, ba ku kuma tuna da ni ba balle ku yi tunanin wannan a zukatanku? Ba don na daɗe ina shiru ba ne ya sa ba kwa tsorona?
Et de qui as-tu eu peur, qui as-tu craint, que tu m'aies menti, et que tu ne te sois point souvenue de moi, [et] que tu ne t'en sois point souciée? Est-ce que je me suis tu; même de si longtemps, que tu ne m'aies point craint?
12 Zan bayyana adalcinku da kuma ayyukanku, ba kuwa za su amfane ku ba.
Je déclarerai ta justice et tes œuvres, qui ne te profiteront point.
13 Sa’ad da kuka nemi taimako, bari tarin gumakanku su cece ku! Iska za tă kwashe dukansu tă tafi, ɗan numfashi kawai zai hura su. Amma mutumin da ya mai da ni mafakarsa zai gāji ƙasar ya kuma mallaki dutsena mai tsarki.”
Que ceux que tu assembles te délivrent, quand tu crieras; mais le vent les enlèvera tous, la vanité les emportera; mais celui qui se retire vers moi héritera la terre, et possédera la montagne de ma sainteté.
14 Za a kuma ce, “Ku gina, ku gina, ku gyara hanya! Ku kawar da abubuwan sa tuntuɓe a hanyar mutanena.”
Et on dira; relevez, relevez, préparez les chemins, ôtez les empêchements loin du chemin de mon peuple.
15 Gama abin da Maɗaukaki da kuma Mai daraja ya faɗa wanda yake raye har abada, wanda sunansa mai tsarki ne, “Ina zama a bisa da kuma a tsattsarkan wuri, amma kuma tare da shi wanda yake mai halin tuba mai tawali’u a ruhu, don in farfaɗo da ruhu mai tawali’u in kuma farfaɗo da zuciyar mai halin tuba.
Car ainsi a dit celui qui est haut et élevé, qui habite dans l'éternité et duquel le nom est le Saint; j'habiterai dans le lieu haut et Saint, et avec celui qui a [le cœur] brisé, et qui est humble d'esprit, afin de vivifier l'esprit des humbles, et afin de vivifier ceux qui ont le cœur brisé.
16 Ba zan tuhume su har abada ba, ba kuwa kullum zai yi fushi ba, gama a haka ruhun mutumin zan yi suma a gabana, shi numfashin mutumin da na halitta.
Parce que je ne débattrai point à toujours, et que je ne serai point indigné à jamais; car c'est de par moi que l'esprit se revêt, et c'est moi qui ai fait les âmes.
17 Na yi fushi saboda kwaɗayin zunubinsa; na yi masa horo, na kuma ɓoye fuskata saboda fushi, duk da haka ya ci gaba da ayyukan zunubinsa.
A cause de l'iniquité de son gain déshonnête j'ai été indigné, et je l'ai frappé; j'ai caché [ma face], et j'ai été indigné; mais le revêche s'en est allé, [et a suivi] la voie de son cœur.
18 Na ga al’amuransa, amma zan warkar da shi; zan bi da shi in mayar da ta’aziyya a gare shi,
J'ai vu ses voies, et toutefois je l'ai guéri; je l'ai ramené, et je lui ai rendu ses consolations, [savoir], à ceux d'entre eux qui mènent deuil.
19 ina ƙirƙiro yabo a leɓunan masu makoki a Isra’ila. Salama, salama, ga waɗanda suke nesa da kuma kusa,” in ji Ubangiji. “Zan kuma warkar da su.”
Je crée ce qui est proféré par les lèvres; paix, paix à celui qui est loin, et à celui qui est près, a dit l'Eternel, car je le guérirai.
20 Amma mugaye suna kama da tumbatsar teku, wanda ba ya natsuwa, wanda raƙumansa sukan kawo gurɓacewa da tabo.
Mais les méchants sont comme la mer qui est dans la tourmente, quand elle ne se peut apaiser; et ses eaux jettent de la bourbe et du limon.
21 “Babu salama ga mugaye,” in ji Allahna.
Il n'y a point de paix pour les méchants, a dit mon Dieu.