< Ishaya 57 >
1 Mai adalci yakan mutu, ba kuwa wanda yakan yi tunani a zuciyarsa; an kwashe mutanen kirki, ba kuwa wanda ya fahimta cewa an kwashe masu adalci don a tsame su daga mugunta.
Le juste périt et personne ne le prend à cœur, les hommes de bien sont enlevés, et nul ne s’avise que c’est à cause de la perversité régnante que le juste disparaît.
2 Waɗanda suke aikata abin da yake daidai sukan shiga da salama; sukan huta yayinda suka kwanta cikin kabari.
Il entre dans la paix, repose sur sa couche, celui qui suit son droit chemin.
3 “Amma ku, ku matso nan, ku’ya’ya maza na masu sihiri, ku zuriyar mazinata da karuwai!
Mais vous, approchez-vous d’ici, enfants de la magicienne, race issue d’un père adultère et d’une mère prostituée!
4 Wane ne kuke yi wa ba’a? Ga wa kuke masa gwalo kuna kuma fitar da harshe? Ashe, ku ba tarin’yan tawaye ba ne, zuriyar maƙaryata?
Contre qui dirigez-vous vos railleries? Contre qui ouvrez-vous une large bouche et tirez-vous la langue? Vous êtes bien les enfants du péché, une lignée de mensonge.
5 Kuna cike da muguwar sha’awa mai ƙonawa a cikin itatuwan oak da kuma a ƙarƙashin kowane itace mai inuwa; kuna miƙa hadayar’ya’yanku a rafuffuka da kuma a ƙarƙashin tsagaggun duwatsu.
Vous vous enflammez dans les bocages, sous chaque arbre verdoyant; vous égorgez les enfants dans les ravins, sous les pointes des rochers!
6 Gumakan da suke cikin duwatsu masu sulɓi su ne rabonku; su ɗin, su ne rabonku. I, gare su kuka kwarara hadayu na sha kuka kuma miƙa hadayu na gari. Saboda waɗannan abubuwa, zan yi haƙuri?
Tu fixes ton choix sur les pierres polies du torrent: voilà, voilà ton lot! Même à elles tu verses des libations, tu apportes des offrandes: se peut-il que j’en prenne mon parti?
7 Kun yi gadonku a dogayen duwatsu masu tsayi da kuma a tudu mai tsawo; a can kuka haura don ku miƙa hadayunku.
Sur des montagnes hautes et altières, tu établis ta couche; là aussi tu grimpes pour faire des sacrifices.
8 A bayan ƙofofi da madogaran ƙofofi kuka kafa alamun gumakanku. Kuka yashe ni, kuka kware gadonku, kuka kwanta a kansa kuka fadada shi; kuka kuma ƙulla yarjejjeniya da waɗanda kuke ƙaunar gadajensu, kuka dubi tsiraicinsu.
Derrière le battant et le poteau de la porte, tu places l’objet de ton culte; t’éloignant de moi, tu découvres ta couche, tu la places haut et tu l’élargis. Il en est avec qui tu pactises, tu aimes leur commerce, tu saisis toutes les occasions favorables.
9 Kuka tafi wurin Molek da man zaitun kuka kuma riɓaɓɓanya turarenku. Kuka aika jakadunku can da nisa; kuka gangara zuwa cikin kabari kansa! (Sheol )
Tu te présentes au roi avec des présents d’huile, tu prodigues tes parfums, tu envoies tes messagers au loin, tu les fais descendre jusqu’au Cheol. (Sheol )
10 Kuka gaji cikin dukan al’amuranku, amma ba ku iya cewa, ‘Aikin banza ne ba.’ Kuka sami sabuntar ƙarfinku, ta haka ba ku suma ba.
À force de faire du chemin, tu es devenue lasse; tu ne dis pas: "C’En est trop!" Tu as retrouvé la vigueur de ton bras, c’est pourquoi tu n’as pas connu de défaillance.
11 “Wa ya sa ku fargaba, kuna jin tsoro har kuka yi mini ƙarya, ba ku kuma tuna da ni ba balle ku yi tunanin wannan a zukatanku? Ba don na daɗe ina shiru ba ne ya sa ba kwa tsorona?
Mais qui donc crains-tu, qui redoutes-tu pour commettre cette trahison, pour perdre mon souvenir et le chasser de ton cœur? N’Est-ce pas, je gardais le silence, et depuis trop longtemps? C’Est pourquoi tu ne me crains pas!
12 Zan bayyana adalcinku da kuma ayyukanku, ba kuwa za su amfane ku ba.
Je vais proclamer tes mérites, et tes œuvres ne te porteront pas bonheur.
13 Sa’ad da kuka nemi taimako, bari tarin gumakanku su cece ku! Iska za tă kwashe dukansu tă tafi, ɗan numfashi kawai zai hura su. Amma mutumin da ya mai da ni mafakarsa zai gāji ƙasar ya kuma mallaki dutsena mai tsarki.”
Lorsque tu feras entendre tes cris, qu’ils te sauvent, ceux que tu as groupés autour de toi! Mais non, tous tant qu’ils sont, le vent les emporte, un souffle les enlève. Au contraire, celui qui se met sous mon abri sera maître du pays et possédera ma sainte montagne.
14 Za a kuma ce, “Ku gina, ku gina, ku gyara hanya! Ku kawar da abubuwan sa tuntuɓe a hanyar mutanena.”
Et l’on dira: "Nivelez, nivelez, déblayez la route! Enlevez tout obstacle de la voie de mon peuple!"
15 Gama abin da Maɗaukaki da kuma Mai daraja ya faɗa wanda yake raye har abada, wanda sunansa mai tsarki ne, “Ina zama a bisa da kuma a tsattsarkan wuri, amma kuma tare da shi wanda yake mai halin tuba mai tawali’u a ruhu, don in farfaɗo da ruhu mai tawali’u in kuma farfaɗo da zuciyar mai halin tuba.
Car ainsi parle le Dieu très haut et suprême, Celui qui habite l’Eternité et qui a nom le Saint: "Sublime et saint est mon trône! Mais il est aussi dans les cœurs contrits et humbles, pour vivifier l’esprit des humbles, pour ranimer le cœur des affligés.
16 Ba zan tuhume su har abada ba, ba kuwa kullum zai yi fushi ba, gama a haka ruhun mutumin zan yi suma a gabana, shi numfashin mutumin da na halitta.
Non; je ne veux pas disputer sans trêve, être toujours en colère, car l’esprit finirait par s’éteindre devant moi, avec ces âmes que moi-même j’ai créées.
17 Na yi fushi saboda kwaɗayin zunubinsa; na yi masa horo, na kuma ɓoye fuskata saboda fushi, duk da haka ya ci gaba da ayyukan zunubinsa.
C’Est contre sa criminelle cupidité que je me suis irrité; j’ai sévi contre lui en dérobant ma face, en n’écoutant que ma colère, alors que, rebelle, il suivait les caprices de son cœur.
18 Na ga al’amuransa, amma zan warkar da shi; zan bi da shi in mayar da ta’aziyya a gare shi,
J’Ai observé ses voies et je veux le guérir, le guider, lui dispenser la consolation, à lui et à ceux qui sont en deuil à son sujet.
19 ina ƙirƙiro yabo a leɓunan masu makoki a Isra’ila. Salama, salama, ga waɗanda suke nesa da kuma kusa,” in ji Ubangiji. “Zan kuma warkar da su.”
Celui qui crée la parole, fruit des lèvres: "Paix, paix, dit-il, pour qui s’est éloigné comme pour le plus proche! Je le guérirai," ainsi parle l’Eternel.
20 Amma mugaye suna kama da tumbatsar teku, wanda ba ya natsuwa, wanda raƙumansa sukan kawo gurɓacewa da tabo.
Mais les pervers sont comme une mer houleuse, qui ne peut s’apaiser et dont les eaux bouillonnent de limon et de fange.
21 “Babu salama ga mugaye,” in ji Allahna.
Point de paix, dit mon Dieu, pour les méchants!