< Ishaya 57 >

1 Mai adalci yakan mutu, ba kuwa wanda yakan yi tunani a zuciyarsa; an kwashe mutanen kirki, ba kuwa wanda ya fahimta cewa an kwashe masu adalci don a tsame su daga mugunta.
Cependant, le juste disparaît, et personne ne le prend à cœur; les hommes pieux sont enlevés, et nul ne prend garde que le juste a été retiré du malheur,
2 Waɗanda suke aikata abin da yake daidai sukan shiga da salama; sukan huta yayinda suka kwanta cikin kabari.
et qu’il entre dans la paix! Ils reposent sur leurs couches, ceux qui ont suivi le droit chemin!
3 “Amma ku, ku matso nan, ku’ya’ya maza na masu sihiri, ku zuriyar mazinata da karuwai!
Mais vous, approchez ici, fils de la magicienne, race de l’adultère et de la prostituée!
4 Wane ne kuke yi wa ba’a? Ga wa kuke masa gwalo kuna kuma fitar da harshe? Ashe, ku ba tarin’yan tawaye ba ne, zuriyar maƙaryata?
De qui vous moquez-vous? Contre qui ouvrez-vous la bouche, et tirez-vous la langue? N’êtes-vous pas des enfants de prévarication, une race de mensonge?
5 Kuna cike da muguwar sha’awa mai ƙonawa a cikin itatuwan oak da kuma a ƙarƙashin kowane itace mai inuwa; kuna miƙa hadayar’ya’yanku a rafuffuka da kuma a ƙarƙashin tsagaggun duwatsu.
Vous vous échauffez près des térébinthes, sous tout arbre vert! vous égorgez les enfants dans les vallées, sous les grottes des rochers?
6 Gumakan da suke cikin duwatsu masu sulɓi su ne rabonku; su ɗin, su ne rabonku. I, gare su kuka kwarara hadayu na sha kuka kuma miƙa hadayu na gari. Saboda waɗannan abubuwa, zan yi haƙuri?
Ta part est dans les pierres polies du torrent; voilà, voilà ton lot! Tu as été jusqu’à leur verser des libations, à leur présenter des offrandes! Puis-je être satisfait de cela?
7 Kun yi gadonku a dogayen duwatsu masu tsayi da kuma a tudu mai tsawo; a can kuka haura don ku miƙa hadayunku.
Sur une montagne haute et élevée tu as établi ta couche! Et c’est là que tu montes pour faire des sacrifices.
8 A bayan ƙofofi da madogaran ƙofofi kuka kafa alamun gumakanku. Kuka yashe ni, kuka kware gadonku, kuka kwanta a kansa kuka fadada shi; kuka kuma ƙulla yarjejjeniya da waɗanda kuke ƙaunar gadajensu, kuka dubi tsiraicinsu.
Derrière la porte et les poteaux, tu as mis ton mémorial; car, loin de moi, tu découvres ta couche, tu y montes, tu élargis ton lit, et tu leur fixes ton salaire; tu aimes leurs embrassements, tu souilles tes regards!
9 Kuka tafi wurin Molek da man zaitun kuka kuma riɓaɓɓanya turarenku. Kuka aika jakadunku can da nisa; kuka gangara zuwa cikin kabari kansa! (Sheol h7585)
Tu te présentes devant le roi avec de l’huile; tu multiplies tes parfums; tu envoies au loin des messagers; tu t’abaisses jusqu’au schéol. (Sheol h7585)
10 Kuka gaji cikin dukan al’amuranku, amma ba ku iya cewa, ‘Aikin banza ne ba.’ Kuka sami sabuntar ƙarfinku, ta haka ba ku suma ba.
A force de démarches, tu te fatigues; tu ne dis pas: « C’est en vain! » tu trouves encore de la vigueur dans ta main; c’est pourquoi tu ne te sens pas malade.
11 “Wa ya sa ku fargaba, kuna jin tsoro har kuka yi mini ƙarya, ba ku kuma tuna da ni ba balle ku yi tunanin wannan a zukatanku? Ba don na daɗe ina shiru ba ne ya sa ba kwa tsorona?
Et qui donc crains-tu? De qui as-tu peur, que tu me sois infidèle, que tu ne te souviennes plus de moi, que tu ne t’en soucies pas? Ne me suis-je pas tu, et depuis longtemps, tandis que tu ne me craignais pas?
12 Zan bayyana adalcinku da kuma ayyukanku, ba kuwa za su amfane ku ba.
Moi, je publierai ta justice, et tes œuvres qui ne te servent de rien.
13 Sa’ad da kuka nemi taimako, bari tarin gumakanku su cece ku! Iska za tă kwashe dukansu tă tafi, ɗan numfashi kawai zai hura su. Amma mutumin da ya mai da ni mafakarsa zai gāji ƙasar ya kuma mallaki dutsena mai tsarki.”
Quand tu crieras, qu’ils te délivrent, tes tas de dieux! Le vent les emportera tous, un souffle les enlèvera! Mais celui qui se confie en moi héritera le pays, et possédera ma sainte montagne.
14 Za a kuma ce, “Ku gina, ku gina, ku gyara hanya! Ku kawar da abubuwan sa tuntuɓe a hanyar mutanena.”
Et l’on dira: Frayez, frayez la voie; aplanissez-la! Enlevez tout obstacle du chemin de mon peuple!
15 Gama abin da Maɗaukaki da kuma Mai daraja ya faɗa wanda yake raye har abada, wanda sunansa mai tsarki ne, “Ina zama a bisa da kuma a tsattsarkan wuri, amma kuma tare da shi wanda yake mai halin tuba mai tawali’u a ruhu, don in farfaɗo da ruhu mai tawali’u in kuma farfaɗo da zuciyar mai halin tuba.
Car ainsi parle le Très-Haut, qui habite une demeure éternelle et s’appelle le Saint: J’habite dans un lieu haut et saint, et en même temps avec l’homme contrit et humble d’esprit, pour rendre la vie à l’esprit des humbles, pour rendre la vie aux cœurs contrits.
16 Ba zan tuhume su har abada ba, ba kuwa kullum zai yi fushi ba, gama a haka ruhun mutumin zan yi suma a gabana, shi numfashin mutumin da na halitta.
Car je ne veux pas contester à jamais, ni garder un courroux éternel; car devant moi tomberaient en défaillance l’esprit et les âmes que j’ai faites.
17 Na yi fushi saboda kwaɗayin zunubinsa; na yi masa horo, na kuma ɓoye fuskata saboda fushi, duk da haka ya ci gaba da ayyukan zunubinsa.
A cause de sa convoitise coupable, je me suis irrité, et, demeurant caché, je l’ai frappé dans mon courroux; et lui, rebelle, suivait la voie de son propre cœur! …
18 Na ga al’amuransa, amma zan warkar da shi; zan bi da shi in mayar da ta’aziyya a gare shi,
J’ai vu ses voies, et je le guérirai; Je serai son guide et je lui rendrai mes consolations, à lui et à ses affligés.
19 ina ƙirƙiro yabo a leɓunan masu makoki a Isra’ila. Salama, salama, ga waɗanda suke nesa da kuma kusa,” in ji Ubangiji. “Zan kuma warkar da su.”
Celui qui crée sur les lèvres la louange, dit: « Paix, paix, à qui est loin et à qui est près, dit Yahweh, et je le guérirai! »
20 Amma mugaye suna kama da tumbatsar teku, wanda ba ya natsuwa, wanda raƙumansa sukan kawo gurɓacewa da tabo.
Mais les méchants sont comme la mer agitée, qui ne peut se calmer, et ses flots roulent de la vase et de la boue.
21 “Babu salama ga mugaye,” in ji Allahna.
Il n’y a pas de paix, dit mon Dieu, pour les méchants.

< Ishaya 57 >