< Ishaya 56 >
1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku riƙe gaskiya ku yi abin da yake daidai, gama cetona yana kusa za a kuma bayyana adalcina nan da nan.
Tako govori Gospod: »Varujte sodbo in ravnajte pravično, kajti moja rešitev duš je blizu, da pride in moja pravičnost, da se razodene.
2 Mai albarka ne mutumin da ya aikata wannan, mutumin da ya riƙe kam yana kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba, yana kuma kiyaye kansa daga yin mugun abu.”
Blagoslovljen je človek, ki to počne in človeški sin, ki se tega oprime, ki varuje šabat pred omadeževanjem in zadržuje svojo roko pred početjem kakršnega koli zla.
3 Kada baƙon da ya miƙa kansa ga Ubangiji ya ce, “Ai Ubangiji zai ware ni daga mutanensa.” Kada kuma wani bābā ya yi gunaguni cewa, “Ni busasshen itace ne kawai.”
Niti ne pusti sinu tujca, ki se je pridružil Gospodu, govoriti, rekoč: › Gospod me je popolnoma ločil od svojega ljudstva.‹ Niti naj evnuh ne reče: ›Glej, jaz sem suho drevo.‹
4 Gama ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Wa bābānnin da suna kiyaye Asabbatai, waɗanda suka zaɓi yin abin da ya gamshe ni suna kuma riƙe da alkawarina kankan,
Kajti tako govori Gospod evnuhom, ki se držijo mojih šabat in izbirajo stvari, ki mi ugajajo in se držijo moje zaveze;
5 a gare su cikin haikalina da kuma bangayensa zan ba da matuni da kuma suna mafi kyau fiye da’ya’ya maza da kuma’ya’ya mata; zan ba su madawwamin sunan da ba za a raba su da shi ba.
celo njim bom dal, v svoji hiši in znotraj svojih zidov, prostor in ime, boljše kakor od sinov in hčera. Dal jim bom večno ime, ki ne bo iztrebljeno.
6 Baƙin da suka miƙa kansu ga Ubangiji don su bauta masa, su kuma ƙaunaci sunan Ubangiji, waɗanda kuma suke yin masa sujada, duk waɗanda suka kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba suka kuma riƙe alkawarina kankan,
Tudi sinove tujca, ki se pridružijo Gospodu, da bi mu služili in da bi ljubili Gospodovo ime, da bi bili njegovi služabniki, vsak, kdor ohranja šabat pred tem, da bi ga omadeževal in se drži moje zaveze,
7 waɗannan ne zan kai tsattsarkan dutsena in sa su yi farin ciki a gidana na addu’a. Hadayunsu na ƙonawa da sadakokinsu za su zama abin karɓa a bagadena; gama za a ce da gidana gidan addu’a domin dukan al’ummai.”
celó pripeljal jih bom na svojo sveto goro in jih razveselil v svoji hiši molitve. Njihove žgalne daritve in njihove klavne daritve bodo sprejete na mojem oltarju, kajti moja hiša se bo imenovala hiša molitve za vsa ljudstva.‹«
8 Ubangiji Mai Iko Duka ya furta cewa, zai tattara korarru na Isra’ila, “Zan ƙara tattaro waɗansu bayan waɗanda na riga na tattara.”
Gospod Bog, ki zbira Izraelove pregnance, govori: »Še bom zbral k njemu druge, poleg tistih, ki so zbrani k njemu.
9 Ku zo, dukanku namun jeji, ku zo ku ci, dukanku namun jeji!
Vse ve poljske živali, pridite, da požrete, da, vse ve živali v gozdu.
10 Matsaran Isra’ila makafi ne, dukansu jahilai ne; dukansu bebayen karnuka ne ba za su iya haushi ba; suna kwance ne kawai suna mafarki, suna son barci ba dama.
Njegovi stražarji so slepi. Vsi so nevedni, vsi so nemi psi, ne morejo lajati; spijo, legajo, radi dremajo.
11 Su karnuka ne masu kwaɗayi; ba su taɓa ƙoshi. Su makiyaya ne marasa ganewa; duk sun nufi inda suka ga dama, kowa yana nemar wa kansa riba.
Da, pohlepni psi so, ki nikoli ne morejo imeti dovolj in pastirji, ki ne morejo razumeti. Vsi gledajo na svojo lastno pot, vsak za svojim dobičkom, od svoje meje.
12 Kowanne yakan ce, “Zo, bari in samo ruwan inabi! Bari mu cika cikinmu da barasa! Gobe ma zai zama kamar yau, ko ma fiye da haka.”
Pridite, pravijo: ›Šel bom po vino in nalili se bomo z močno pijačo in jutrišnji dan bo kakor ta dan in mnogo obilnejši.‹«