< Ishaya 56 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku riƙe gaskiya ku yi abin da yake daidai, gama cetona yana kusa za a kuma bayyana adalcina nan da nan.
Nanku okutshiwo nguThixo: “Londoloza ukulunga wenze okuqondileyo, ngoba ukusindisa kwami kuseduze lokulunga kwami kuzabonakaliswa masinyane.
2 Mai albarka ne mutumin da ya aikata wannan, mutumin da ya riƙe kam yana kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba, yana kuma kiyaye kansa daga yin mugun abu.”
Ubusisiwe umuntu okwenzayo lokhu, umuntu obambelela kukho, ogcina iSabatha engalingcolisi, athibe isandla sakhe ekwenzeni okubi.”
3 Kada baƙon da ya miƙa kansa ga Ubangiji ya ce, “Ai Ubangiji zai ware ni daga mutanensa.” Kada kuma wani bābā ya yi gunaguni cewa, “Ni busasshen itace ne kawai.”
Akungabi lowezizweni okuThixo othi, “Ngeqiniso uThixo uzangehlukanisa labantu bakhe.” Njalo lomthenwa kangavunyelwa ukusola athi, “Mina ngiyisihlahla esomileyo.”
4 Gama ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Wa bābānnin da suna kiyaye Asabbatai, waɗanda suka zaɓi yin abin da ya gamshe ni suna kuma riƙe da alkawarina kankan,
Ngoba uThixo uthi: “Abathenwa abagcina amaSabatha ami bakhethe okungithokozisayo, babambelele kusivumelwano sami,
5 a gare su cikin haikalina da kuma bangayensa zan ba da matuni da kuma suna mafi kyau fiye da’ya’ya maza da kuma’ya’ya mata; zan ba su madawwamin sunan da ba za a raba su da shi ba.
ngizabanika, phakathi kwethempeli lami lemiduli yalo, isikhumbuzo lebizo elingcono kulamadodana lamadodakazi. Ngizabanika ibizo elingapheliyo. Elingayikukhohlakala.
6 Baƙin da suka miƙa kansu ga Ubangiji don su bauta masa, su kuma ƙaunaci sunan Ubangiji, waɗanda kuma suke yin masa sujada, duk waɗanda suka kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba suka kuma riƙe alkawarina kankan,
Labezizwe abazinikela kuThixo ukuba bamkhonze, bathande ibizo likaThixo, njalo bamkhonze, bonke abagcina iSabatha bengalingcolisi, babambelele kusivumelwano sami,
7 waɗannan ne zan kai tsattsarkan dutsena in sa su yi farin ciki a gidana na addu’a. Hadayunsu na ƙonawa da sadakokinsu za su zama abin karɓa a bagadena; gama za a ce da gidana gidan addu’a domin dukan al’ummai.”
laba ngizabaletha entabeni yami engcwele, ngibaphe intokozo endlini yami yokukhulekela. Iminikelo yabo yokutshiswa, lemihlatshelo, kuzakwamukelwa e-alithareni lami; ngoba indlu yami izathiwa yindlu yokukhuleka yezizwe zonke.”
8 Ubangiji Mai Iko Duka ya furta cewa, zai tattara korarru na Isra’ila, “Zan ƙara tattaro waɗansu bayan waɗanda na riga na tattara.”
UThixo Wobukhosi, yena oqoqa abaxotshwayo elizweni abako-Israyeli uthi: “Ngizaqoqela abanye kubo futhi ngaphandle kwalabo abavele sebeqoqiwe.”
9 Ku zo, dukanku namun jeji, ku zo ku ci, dukanku namun jeji!
Wozani lonke lina zilo zeganga; wozani lidle, lonke lina zilo zamagusu!
10 Matsaran Isra’ila makafi ne, dukansu jahilai ne; dukansu bebayen karnuka ne ba za su iya haushi ba; suna kwance ne kawai suna mafarki, suna son barci ba dama.
Abalindi bako-Israyeli bayiziphofu, bonke kabazi lutho; bonke bayimigaxa, izinja ezingakhonkothiyo; balala nje baphuphe; bathanda ukulala.
11 Su karnuka ne masu kwaɗayi; ba su taɓa ƙoshi. Su makiyaya ne marasa ganewa; duk sun nufi inda suka ga dama, kowa yana nemar wa kansa riba.
Bayizinja ezihlala zilomdlozela wokufuna ukudla, azisuthi. Bangabelusi abangaqedisisiyo, bonke bazazenzela abakufunayo, lowo lalowo udinga inzuzo yakhe.
12 Kowanne yakan ce, “Zo, bari in samo ruwan inabi! Bari mu cika cikinmu da barasa! Gobe ma zai zama kamar yau, ko ma fiye da haka.”
Lowo lalowo uthi, “Wozani, ngilethe iwayini. Kasinatheni utshwala sibusuthe. Kusasa kuzafana lanamuhla, loba kube ngcono kakhulu.”

< Ishaya 56 >