< Ishaya 56 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku riƙe gaskiya ku yi abin da yake daidai, gama cetona yana kusa za a kuma bayyana adalcina nan da nan.
Voici ce que dit le Seigneur: Gardez le jugement et pratiquez la justice; parce que mon salut est près de venir, et ma justice, d’être révélée.
2 Mai albarka ne mutumin da ya aikata wannan, mutumin da ya riƙe kam yana kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba, yana kuma kiyaye kansa daga yin mugun abu.”
Bienheureux l’homme qui observe ceci, et le fils de l’homme qui s’y attachera; gardant le sabbat, afin de ne pas le profaner, gardant ses mains, afin de ne faire aucun mal.
3 Kada baƙon da ya miƙa kansa ga Ubangiji ya ce, “Ai Ubangiji zai ware ni daga mutanensa.” Kada kuma wani bābā ya yi gunaguni cewa, “Ni busasshen itace ne kawai.”
Et qu’il ne dise en aucune manière, le fils de l’étranger qui s’attache au Seigneur: Le Seigneur me séparera entièrement de son peuple. Et que l’eunuque ne dise pas: Voici que je suis un bois aride.
4 Gama ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Wa bābānnin da suna kiyaye Asabbatai, waɗanda suka zaɓi yin abin da ya gamshe ni suna kuma riƙe da alkawarina kankan,
Parce que voici ce que dit le Seigneur aux eunuques: Ceux qui gardent mes sabbats, et qui choisissent ce que je veux et observent mon alliance;
5 a gare su cikin haikalina da kuma bangayensa zan ba da matuni da kuma suna mafi kyau fiye da’ya’ya maza da kuma’ya’ya mata; zan ba su madawwamin sunan da ba za a raba su da shi ba.
Je leur donnerai dans ma maison et dans mes murs un lieu et un nom plus avantageux que des fils et des filles; je leur donnerai un nom éternel qui ne périra pas.
6 Baƙin da suka miƙa kansu ga Ubangiji don su bauta masa, su kuma ƙaunaci sunan Ubangiji, waɗanda kuma suke yin masa sujada, duk waɗanda suka kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba suka kuma riƙe alkawarina kankan,
Et les fils de l’étranger qui s’attachent au Seigneur, afin de l’adorer et d’aimer son nom, afin d’être ses serviteurs, et tous ceux qui gardent le sabbat pour ne pas le profaner, et observent mon alliance,
7 waɗannan ne zan kai tsattsarkan dutsena in sa su yi farin ciki a gidana na addu’a. Hadayunsu na ƙonawa da sadakokinsu za su zama abin karɓa a bagadena; gama za a ce da gidana gidan addu’a domin dukan al’ummai.”
Je les conduirai sur ma montagne sainte, je les remplirai de joie dans ma maison de prière; leurs holocaustes et leurs victimes, offerts sur mon autel, me seront agréables; parce que ma maison sera appelée maison de prière pour tous les peuples.
8 Ubangiji Mai Iko Duka ya furta cewa, zai tattara korarru na Isra’ila, “Zan ƙara tattaro waɗansu bayan waɗanda na riga na tattara.”
Le Seigneur Dieu, qui rassemble les dispersés d’Israël, dit: Je réunirai encore à lui ceux qui se joindront à lui.
9 Ku zo, dukanku namun jeji, ku zo ku ci, dukanku namun jeji!
Vous toutes, bêtes des champs, vous toutes, bêtes des forêts, venez pour dévorer.
10 Matsaran Isra’ila makafi ne, dukansu jahilai ne; dukansu bebayen karnuka ne ba za su iya haushi ba; suna kwance ne kawai suna mafarki, suna son barci ba dama.
Ses sentinelles sont toutes aveugles; elles sont toutes dans l’ignorance; des chiens muets, qui ne peuvent aboyer, qui voient des fantômes, qui dorment et qui aiment les songes.
11 Su karnuka ne masu kwaɗayi; ba su taɓa ƙoshi. Su makiyaya ne marasa ganewa; duk sun nufi inda suka ga dama, kowa yana nemar wa kansa riba.
Et ces chiens d’une impudence extrême n’ont pas connu le rassasiement; les pasteurs eux-mêmes n’ont pas d’intelligence; tous se sont détournés vers leur voie, chacun vers son avarice, depuis le plus grand jusqu’au plus petit.
12 Kowanne yakan ce, “Zo, bari in samo ruwan inabi! Bari mu cika cikinmu da barasa! Gobe ma zai zama kamar yau, ko ma fiye da haka.”
Venez, disent-ils, prenons du vin, remplissons-nous-en jusqu’à l’ivresse; et comme aujourd’hui, ainsi il en sera demain, et beaucoup plus encore.

< Ishaya 56 >