< Ishaya 56 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku riƙe gaskiya ku yi abin da yake daidai, gama cetona yana kusa za a kuma bayyana adalcina nan da nan.
Yahvé dit: « Maintenir la justice et faire ce qui est juste, car mon salut est proche et ma justice sera bientôt révélée.
2 Mai albarka ne mutumin da ya aikata wannan, mutumin da ya riƙe kam yana kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba, yana kuma kiyaye kansa daga yin mugun abu.”
Béni soit l'homme qui fait cela, et le fils de l'homme qui la retient; qui garde le sabbat sans le profaner et empêche sa main de faire le mal. »
3 Kada baƙon da ya miƙa kansa ga Ubangiji ya ce, “Ai Ubangiji zai ware ni daga mutanensa.” Kada kuma wani bābā ya yi gunaguni cewa, “Ni busasshen itace ne kawai.”
Que l'étranger qui s'est uni à Yahvé ne parle pas en disant, « Yahvé me séparera de son peuple. » Ne laissez pas l'eunuque dire: « Voici, je suis un arbre sec. »
4 Gama ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Wa bābānnin da suna kiyaye Asabbatai, waɗanda suka zaɓi yin abin da ya gamshe ni suna kuma riƙe da alkawarina kankan,
Car Yahvé dit: « Aux eunuques qui observent mes sabbats, choisir les choses qui me plaisent, et attachez-vous à mon alliance,
5 a gare su cikin haikalina da kuma bangayensa zan ba da matuni da kuma suna mafi kyau fiye da’ya’ya maza da kuma’ya’ya mata; zan ba su madawwamin sunan da ba za a raba su da shi ba.
Je leur donnerai dans ma maison et dans mes murs un souvenir et un nom meilleurs que ceux des fils et des filles. Je leur donnerai un nom éternel qui ne sera pas supprimé.
6 Baƙin da suka miƙa kansu ga Ubangiji don su bauta masa, su kuma ƙaunaci sunan Ubangiji, waɗanda kuma suke yin masa sujada, duk waɗanda suka kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba suka kuma riƙe alkawarina kankan,
De même, les étrangers qui s'attachent à Yahvé pour le servir, et d'aimer le nom de Yahvé, pour être ses serviteurs, tous ceux qui observent le sabbat ne le profanent pas, et tient fermement mon alliance,
7 waɗannan ne zan kai tsattsarkan dutsena in sa su yi farin ciki a gidana na addu’a. Hadayunsu na ƙonawa da sadakokinsu za su zama abin karɓa a bagadena; gama za a ce da gidana gidan addu’a domin dukan al’ummai.”
Je les amènerai sur ma montagne sainte, et les rendre joyeux dans ma maison de prière. Leurs holocaustes et leurs sacrifices seront acceptés sur mon autel; car ma maison sera appelée une maison de prière pour tous les peuples. »
8 Ubangiji Mai Iko Duka ya furta cewa, zai tattara korarru na Isra’ila, “Zan ƙara tattaro waɗansu bayan waɗanda na riga na tattara.”
Le Seigneur Yahvé, qui rassemble les exclus d'Israël, dit, « Je vais encore en rassembler d'autres auprès de lui, en plus des siens qui sont réunis. »
9 Ku zo, dukanku namun jeji, ku zo ku ci, dukanku namun jeji!
Vous tous, animaux des champs, venir pour dévorer, tous les animaux de la forêt.
10 Matsaran Isra’ila makafi ne, dukansu jahilai ne; dukansu bebayen karnuka ne ba za su iya haushi ba; suna kwance ne kawai suna mafarki, suna son barci ba dama.
Ses gardiens sont aveugles. Ils sont tous sans connaissance. Ce sont tous des chiens muets. Ils ne peuvent pas aboyer... rêver, s'allonger, aimer s'assoupir.
11 Su karnuka ne masu kwaɗayi; ba su taɓa ƙoshi. Su makiyaya ne marasa ganewa; duk sun nufi inda suka ga dama, kowa yana nemar wa kansa riba.
Oui, les chiens sont gourmands. Ils n'en ont jamais assez. Ce sont des bergers qui ne peuvent pas comprendre. Ils se sont tous tournés vers leur propre voie, chacun à son profit, de tous les côtés.
12 Kowanne yakan ce, “Zo, bari in samo ruwan inabi! Bari mu cika cikinmu da barasa! Gobe ma zai zama kamar yau, ko ma fiye da haka.”
« Viens, disent-ils, je vais chercher du vin, et nous nous remplirons de boissons fortes; et demain sera comme aujourd'hui, grand au-delà de toute mesure. »

< Ishaya 56 >