< Ishaya 56 >
1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku riƙe gaskiya ku yi abin da yake daidai, gama cetona yana kusa za a kuma bayyana adalcina nan da nan.
Thus he says Yahweh keep justice and do righteousness for [is] near salvation my to come and righteousness my to be revealed.
2 Mai albarka ne mutumin da ya aikata wannan, mutumin da ya riƙe kam yana kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba, yana kuma kiyaye kansa daga yin mugun abu.”
How blessed! [is the] person [who] he does this and [the] child of humankind [who] he takes hold on it [who] keeps [the] sabbath from profaning it and [who] keeps hand his from doing any evil.
3 Kada baƙon da ya miƙa kansa ga Ubangiji ya ce, “Ai Ubangiji zai ware ni daga mutanensa.” Kada kuma wani bābā ya yi gunaguni cewa, “Ni busasshen itace ne kawai.”
And may not he say [the] son of foreignness who has joined himself to Yahweh saying certainly he will separate me Yahweh from with people his and may not he say the eunuch here! I [am] a tree dry.
4 Gama ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Wa bābānnin da suna kiyaye Asabbatai, waɗanda suka zaɓi yin abin da ya gamshe ni suna kuma riƙe da alkawarina kankan,
For thus - he says Yahweh to the eunuchs who they keep sabbaths my and they choose [that] which I desire and [they are] keeping hold on covenant my.
5 a gare su cikin haikalina da kuma bangayensa zan ba da matuni da kuma suna mafi kyau fiye da’ya’ya maza da kuma’ya’ya mata; zan ba su madawwamin sunan da ba za a raba su da shi ba.
And I will give to them in house my and in walls my a monument and a name good more than sons and more than daughters a name of perpetuity I will give to him which not it will be cut off.
6 Baƙin da suka miƙa kansu ga Ubangiji don su bauta masa, su kuma ƙaunaci sunan Ubangiji, waɗanda kuma suke yin masa sujada, duk waɗanda suka kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba suka kuma riƙe alkawarina kankan,
And [the] sons of foreignness who join themselves to Yahweh to serve him and to love [the] name of Yahweh to become of him servants every [one who] keeps [the] sabbath from profaning it and [those who] keep hold on covenant my.
7 waɗannan ne zan kai tsattsarkan dutsena in sa su yi farin ciki a gidana na addu’a. Hadayunsu na ƙonawa da sadakokinsu za su zama abin karɓa a bagadena; gama za a ce da gidana gidan addu’a domin dukan al’ummai.”
And I will bring them to [the] mountain of holiness my and I will make rejoice them in [the] house of prayer my burnt offerings their and sacrifices their [will be] for acceptance on altar my for house my a house of prayer it will be called for all the peoples.
8 Ubangiji Mai Iko Duka ya furta cewa, zai tattara korarru na Isra’ila, “Zan ƙara tattaro waɗansu bayan waɗanda na riga na tattara.”
[the] utterance of [the] Lord Yahweh [who] gathers [the] banished [ones] of Israel still I will gather to it to gathered [ones] its.
9 Ku zo, dukanku namun jeji, ku zo ku ci, dukanku namun jeji!
O every animal of [the] field come to devour O every animal in the forest.
10 Matsaran Isra’ila makafi ne, dukansu jahilai ne; dukansu bebayen karnuka ne ba za su iya haushi ba; suna kwance ne kawai suna mafarki, suna son barci ba dama.
(Watchmen its *Q(K)*) [are] blind all of them not they know all of them [are] dogs dumb not they are able to bark [they] dream [they] lie down [they] love to slumber.
11 Su karnuka ne masu kwaɗayi; ba su taɓa ƙoshi. Su makiyaya ne marasa ganewa; duk sun nufi inda suka ga dama, kowa yana nemar wa kansa riba.
And the dogs [are] mighty of appetite not they know satiety and they [are] shepherds not they know to understand all of them to own way their they have turned everyone to own unjust gain his from end his.
12 Kowanne yakan ce, “Zo, bari in samo ruwan inabi! Bari mu cika cikinmu da barasa! Gobe ma zai zama kamar yau, ko ma fiye da haka.”
Come let me take wine and let us drink strong drink and it will be like this day tomorrow great abundance exceedingly.