< Ishaya 56 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku riƙe gaskiya ku yi abin da yake daidai, gama cetona yana kusa za a kuma bayyana adalcina nan da nan.
Thus saith the LORD: Keep ye justice, and do righteousness; for My salvation is near to come, and My favour to be revealed.
2 Mai albarka ne mutumin da ya aikata wannan, mutumin da ya riƙe kam yana kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba, yana kuma kiyaye kansa daga yin mugun abu.”
Happy is the man that doeth this, and the son of man that holdeth fast by it: that keepeth the sabbath from profaning it, and keepeth his hand from doing any evil.
3 Kada baƙon da ya miƙa kansa ga Ubangiji ya ce, “Ai Ubangiji zai ware ni daga mutanensa.” Kada kuma wani bābā ya yi gunaguni cewa, “Ni busasshen itace ne kawai.”
Neither let the alien, that hath joined himself to the LORD, speak, saying: 'The LORD will surely separate me from His people'; neither let the eunuch say: 'Behold, I am a dry tree.'
4 Gama ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Wa bābānnin da suna kiyaye Asabbatai, waɗanda suka zaɓi yin abin da ya gamshe ni suna kuma riƙe da alkawarina kankan,
For thus saith the LORD concerning the eunuchs that keep My sabbaths, and choose the things that please Me, and hold fast by My covenant:
5 a gare su cikin haikalina da kuma bangayensa zan ba da matuni da kuma suna mafi kyau fiye da’ya’ya maza da kuma’ya’ya mata; zan ba su madawwamin sunan da ba za a raba su da shi ba.
Even unto them will I give in My house and within My walls a monument and a memorial better than sons and daughters; I will give them an everlasting memorial, that shall not be cut off.
6 Baƙin da suka miƙa kansu ga Ubangiji don su bauta masa, su kuma ƙaunaci sunan Ubangiji, waɗanda kuma suke yin masa sujada, duk waɗanda suka kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba suka kuma riƙe alkawarina kankan,
Also the aliens, that join themselves to the LORD, to minister unto Him, and to love the name of the LORD, to be His servants, every one that keepeth the sabbath from profaning it, and holdeth fast by My covenant:
7 waɗannan ne zan kai tsattsarkan dutsena in sa su yi farin ciki a gidana na addu’a. Hadayunsu na ƙonawa da sadakokinsu za su zama abin karɓa a bagadena; gama za a ce da gidana gidan addu’a domin dukan al’ummai.”
Even them will I bring to My holy mountain, and make them joyful in My house of prayer; their burnt-offerings and their sacrifices shall be acceptable upon Mine altar; for My house shall be called a house of prayer for all peoples.
8 Ubangiji Mai Iko Duka ya furta cewa, zai tattara korarru na Isra’ila, “Zan ƙara tattaro waɗansu bayan waɗanda na riga na tattara.”
Saith the Lord GOD who gathereth the dispersed of Israel: Yet I will gather others to him, beside those of him that are gathered.
9 Ku zo, dukanku namun jeji, ku zo ku ci, dukanku namun jeji!
All ye beasts of the field, come to devour, yea, all ye beasts in the forest.
10 Matsaran Isra’ila makafi ne, dukansu jahilai ne; dukansu bebayen karnuka ne ba za su iya haushi ba; suna kwance ne kawai suna mafarki, suna son barci ba dama.
His watchmen are all blind, without knowledge; they are all dumb dogs, they cannot bark; raving, lying down, loving to slumber.
11 Su karnuka ne masu kwaɗayi; ba su taɓa ƙoshi. Su makiyaya ne marasa ganewa; duk sun nufi inda suka ga dama, kowa yana nemar wa kansa riba.
Yea, the dogs are greedy, they know not when they have enough; and these are shepherds that cannot understand; they all turn to their own way, each one to his gain, one and all.
12 Kowanne yakan ce, “Zo, bari in samo ruwan inabi! Bari mu cika cikinmu da barasa! Gobe ma zai zama kamar yau, ko ma fiye da haka.”
'Come ye, I will fetch wine, and we will fill ourselves with strong drink; and to-morrow shall be as this day, and much more abundant.'

< Ishaya 56 >