< Ishaya 55 >

1 “Ku zo, dukanku masu jin ƙishi, ku zo wurin ruwaye; ku kuma da ba ku da kuɗi, ku zo, ku saya ku kuma ci! Ku zo, ku saya ruwan inabi da madara ba tare da kuɗi ba ba za ku kuma biya kome ba.
Ој жедни који сте год, ходите на воду, и који немате новца, ходите, купујте и једите; ходите, купујте без новца и без плате вино и млеко.
2 Don me za ku kashe kuɗi a kan abin da ba abinci ba, ku kuma yi wahala a kan abin da ba za ku ƙoshi ba? Ku saurara, ku saurare ni, ku kuma ci abin da yake da kyau, ranku kuma zai ji daɗin abinci mafi kyau.
Зашто трошите новце своје на оно што није храна, и труд свој на оно што не сити? Слушајте ме, па ћете јести шта је добро, и душа ће се ваша насладити претилине.
3 Ku kasa kunne ku kuma zo gare ni; ku saurare ni, don ranku ya rayu. Zan yi madawwamin alkawari da ku, zan nuna muku ƙaunata marar ƙarewa da na yi wa Dawuda alkawari.
Пригните ухо своје и ходите к мени; послушајте, и жива ће бити душа ваша, и учинићу с вама завет вечан, милости Давидове истините.
4 Duba, na mai da shi shaida ga mutane, shugaba da kuma jagorar mutane.
Ево, дадох га за сведока народима, за вођу и заповедника народима.
5 Tabbatacce za ku kira al’umman da ba ku sani ba, kuma al’umman da ba ku sani ba za su sheƙo a guje zuwa wurinku, saboda Ubangiji Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya darjanta ku.”
Ево, зваћеш народ који ниси знао, и народи који те нису знали стећи ће се к теби, ради Господа Бога твог и Свеца Израиљевог, јер те прослави.
6 Ku nemi Ubangiji tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.
Тражите Господа, док се може наћи; призивајте Га, докле је близу.
7 Bari mugu ya bar irin halinsa mugu kuma ya sāke irin tunaninsa. Bari yă juyo ga Ubangiji, zai kuwa ji tausayinsa, ya juyo ga Allahnmu kuma, gama shi mai gafartawa ne a sauƙaƙe.
Нека безбожник остави свој пут и неправедник мисли своје; и нека се врати ка Господу, и смиловаћу се на њ, и к Богу нашем, јер прашта много.
8 “Gama tunanina ba tunaninku ba ne, yadda kuke yin abubuwa ba yadda nake yin abubuwa ba ne,” in ji Ubangiji.
Јер мисли моје нису ваше мисли, нити су ваши путеви моји путеви, вели Господ;
9 “Kamar yadda sammai suke can nesa da ƙasa, haka yadda nake yin abubuwa suke dabam da yadda kuke yin abubuwa tunanina kuma dabam da naku.
Него колико су небеса више од земље, толико су путеви моји виши од ваших путева, и мисли моје од ваших мисли.
10 Kamar yadda ruwan sama da dusar ƙanƙara suke saukowa daga sama, ba sa komowa ba tare da sun jiƙe duniya sun kuma sa su yi’ya’ya su kuma yi toho, don su ba da iri ga mai shuki da kuma abinci ga mai ci,
Јер како пада дажд или снег с неба и не враћа се онамо, него натапа земљу и учини да рађа и да се зелени, да даје семе да се сеје и хлеб да се једе,
11 haka maganata da take fitowa daga bakina. Ba za tă koma gare ni wofi ba, amma za tă cika abin da nake so ta kuma cika abin da na aike ta tă yi.
Тако ће бити реч моја кад изађе из мојих уста: неће се вратити к мени празна, него ће учинити шта ми је драго, и срећно ће свршити на шта је пошаљем.
12 Za ku fita da farin ciki a kuma bi da ku da salama; duwatsu da tuddai za su ɓarke da waƙa a gabanku, dukan itatuwan jeji kuma za su tafa hannuwansu.
Јер ћете с весељем изаћи, и у миру ћете бити вођени; горе и брегови певаће пред вама од радости, и сва ће дрвета пољска пљескати рукама.
13 A maimakon sarƙaƙƙiya, itacen fir ne zai tsiro, a maimakon ƙayayyuwa kuma, itacen ci-zaƙi ne zai tsiro. Wannan zai zama matuni na abin da Ni Ubangiji na yi, madawwamiyar alama ce, wadda ba za a datse ba.”
Место трња никнуће јела, место коприве никнуће мирта; и то ће бити Господу у славу, за вечан знак, који неће нестати.

< Ishaya 55 >