< Ishaya 55 >
1 “Ku zo, dukanku masu jin ƙishi, ku zo wurin ruwaye; ku kuma da ba ku da kuɗi, ku zo, ku saya ku kuma ci! Ku zo, ku saya ruwan inabi da madara ba tare da kuɗi ba ba za ku kuma biya kome ba.
Vous tous qui avez soif, venez vers les eaux; et vous qui n’avez pas d’argent, hâtez-vous, achetez et mangez; venez, achetez sans argent et sans aucun échange du vin et du lait.
2 Don me za ku kashe kuɗi a kan abin da ba abinci ba, ku kuma yi wahala a kan abin da ba za ku ƙoshi ba? Ku saurara, ku saurare ni, ku kuma ci abin da yake da kyau, ranku kuma zai ji daɗin abinci mafi kyau.
Pourquoi dépensez-vous de l’argent à ce qui n’est pas du pain, et votre travail à ce qui ne peut vous rassasier? Ecoutez-moi avec une grande attention, et mangez une bonne nourriture, et votre âme se délectera en s’en engraissant.
3 Ku kasa kunne ku kuma zo gare ni; ku saurare ni, don ranku ya rayu. Zan yi madawwamin alkawari da ku, zan nuna muku ƙaunata marar ƙarewa da na yi wa Dawuda alkawari.
Inclinez votre oreille, et venez à moi; écoutez, et votre âme vivra, et je ferai avec vous un pacte éternel qui montrera véritables les miséricordes promises à David.
4 Duba, na mai da shi shaida ga mutane, shugaba da kuma jagorar mutane.
Voilà que je l’ai donné pour témoin aux peuples, pour chef et pour maître aux nations.
5 Tabbatacce za ku kira al’umman da ba ku sani ba, kuma al’umman da ba ku sani ba za su sheƙo a guje zuwa wurinku, saboda Ubangiji Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya darjanta ku.”
Voilà que tu appelleras une nation que tu ne connaissais pas; et des nations qui ne t’ont pas connu vers toi accourront, à cause du Seigneur ton Dieu, et du saint d’Israël qui t’a glorifié.
6 Ku nemi Ubangiji tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.
Cherchez le Seigneur, tandis qu’on peut le trouver, invoquez-le tandis qu’il est proche.
7 Bari mugu ya bar irin halinsa mugu kuma ya sāke irin tunaninsa. Bari yă juyo ga Ubangiji, zai kuwa ji tausayinsa, ya juyo ga Allahnmu kuma, gama shi mai gafartawa ne a sauƙaƙe.
Que l’impie abandonne sa voie, et l’homme inique ses pensées, et qu’il retourne au Seigneur, et il aura pitié de lui; et à notre Dieu, parce qu’il pardonne beaucoup.
8 “Gama tunanina ba tunaninku ba ne, yadda kuke yin abubuwa ba yadda nake yin abubuwa ba ne,” in ji Ubangiji.
Car mes pensées ne sont pas vos pensées, ni vos voies mes voies, dit le Seigneur.
9 “Kamar yadda sammai suke can nesa da ƙasa, haka yadda nake yin abubuwa suke dabam da yadda kuke yin abubuwa tunanina kuma dabam da naku.
Parce qu’autant les cieux sont élevés au-dessus de la terre, autant sont élevées mes voies au-dessus de vos voies, et mes pensées au-dessus de vos pensées.
10 Kamar yadda ruwan sama da dusar ƙanƙara suke saukowa daga sama, ba sa komowa ba tare da sun jiƙe duniya sun kuma sa su yi’ya’ya su kuma yi toho, don su ba da iri ga mai shuki da kuma abinci ga mai ci,
Et de même que la pluie et la neige descendent du ciel et n’y retournent plus, mais qu’elles abreuvent la terre, la pénètrent, la font germer, et qu’elle donnent la semence au semeur, et le pain à celui qui le mange;
11 haka maganata da take fitowa daga bakina. Ba za tă koma gare ni wofi ba, amma za tă cika abin da nake so ta kuma cika abin da na aike ta tă yi.
Ainsi sera ma parole qui sortira de ma bouche; elle ne reviendra pas à moi sans effet; mais elle fera tout ce que j’ai voulu, et elle réussira dans toutes les choses pour lesquelles je l’aurai envoyée.
12 Za ku fita da farin ciki a kuma bi da ku da salama; duwatsu da tuddai za su ɓarke da waƙa a gabanku, dukan itatuwan jeji kuma za su tafa hannuwansu.
Parce que dans la joie vous sortirez, et dans la paix vous serez ramenés; les montagnes et les collines chanteront devant vous des louanges, et tous les arbres du pays battront des mains.
13 A maimakon sarƙaƙƙiya, itacen fir ne zai tsiro, a maimakon ƙayayyuwa kuma, itacen ci-zaƙi ne zai tsiro. Wannan zai zama matuni na abin da Ni Ubangiji na yi, madawwamiyar alama ce, wadda ba za a datse ba.”
Au lieu du nard sauvage s’élèvera le sapin, et au lieu de l’ortie croîtra le myrte; et le nom du Seigneur deviendra un signe éternel, qui ne sera pas enlevé.