< Ishaya 55 >

1 “Ku zo, dukanku masu jin ƙishi, ku zo wurin ruwaye; ku kuma da ba ku da kuɗi, ku zo, ku saya ku kuma ci! Ku zo, ku saya ruwan inabi da madara ba tare da kuɗi ba ba za ku kuma biya kome ba.
All you who thirst, come to the waters. And you who have no money: hurry, buy and eat. Approach, buy wine and milk, without money and without barter.
2 Don me za ku kashe kuɗi a kan abin da ba abinci ba, ku kuma yi wahala a kan abin da ba za ku ƙoshi ba? Ku saurara, ku saurare ni, ku kuma ci abin da yake da kyau, ranku kuma zai ji daɗin abinci mafi kyau.
Why do you spend money for what is not bread, and expend your labor for what does not satisfy? Listen very closely to me, and eat what is good, and then your soul will be delighted by a full measure.
3 Ku kasa kunne ku kuma zo gare ni; ku saurare ni, don ranku ya rayu. Zan yi madawwamin alkawari da ku, zan nuna muku ƙaunata marar ƙarewa da na yi wa Dawuda alkawari.
Incline your ear and draw near to me. Listen, and your soul will live. And I will make an everlasting covenant with you, by the faithful mercies of David.
4 Duba, na mai da shi shaida ga mutane, shugaba da kuma jagorar mutane.
Behold, I have presented him as a witness to the people, as a commander and instructor to the nations.
5 Tabbatacce za ku kira al’umman da ba ku sani ba, kuma al’umman da ba ku sani ba za su sheƙo a guje zuwa wurinku, saboda Ubangiji Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya darjanta ku.”
Behold, you will call to a nation that you did not know. And nations that did not know you will rush to you, because of the Lord your God, the Holy One of Israel. For he has glorified you.
6 Ku nemi Ubangiji tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.
Seek the Lord, while he is able to be found. Call upon him, while he is near.
7 Bari mugu ya bar irin halinsa mugu kuma ya sāke irin tunaninsa. Bari yă juyo ga Ubangiji, zai kuwa ji tausayinsa, ya juyo ga Allahnmu kuma, gama shi mai gafartawa ne a sauƙaƙe.
Let the impious one abandon his way, and the iniquitous man his thoughts, and let him return to the Lord, and he will take pity on him, and to our God, for he is great in forgiveness.
8 “Gama tunanina ba tunaninku ba ne, yadda kuke yin abubuwa ba yadda nake yin abubuwa ba ne,” in ji Ubangiji.
For my thoughts are not your thoughts, and your ways are not my ways, says the Lord.
9 “Kamar yadda sammai suke can nesa da ƙasa, haka yadda nake yin abubuwa suke dabam da yadda kuke yin abubuwa tunanina kuma dabam da naku.
For just as the heavens are exalted above the earth, so also are my ways exalted above your ways, and my thoughts above your thoughts.
10 Kamar yadda ruwan sama da dusar ƙanƙara suke saukowa daga sama, ba sa komowa ba tare da sun jiƙe duniya sun kuma sa su yi’ya’ya su kuma yi toho, don su ba da iri ga mai shuki da kuma abinci ga mai ci,
And in the same manner as rain and snow descend from heaven, and no longer return there, but soak the earth, and water it, and cause it to bloom and to provide seed to the sower and bread to the hungry,
11 haka maganata da take fitowa daga bakina. Ba za tă koma gare ni wofi ba, amma za tă cika abin da nake so ta kuma cika abin da na aike ta tă yi.
so also will my word be, which will go forth from my mouth. It will not return to me empty, but it will accomplish whatever I will, and it will prosper in the tasks for which I sent it.
12 Za ku fita da farin ciki a kuma bi da ku da salama; duwatsu da tuddai za su ɓarke da waƙa a gabanku, dukan itatuwan jeji kuma za su tafa hannuwansu.
For you will go forth rejoicing, and you will be led forward in peace. The mountains and the hills will sing praise before you, and all the trees of the countryside will clap their hands.
13 A maimakon sarƙaƙƙiya, itacen fir ne zai tsiro, a maimakon ƙayayyuwa kuma, itacen ci-zaƙi ne zai tsiro. Wannan zai zama matuni na abin da Ni Ubangiji na yi, madawwamiyar alama ce, wadda ba za a datse ba.”
In place of the shrub, the pine tree will arise, and in place of the nettle, the myrtle tree will grow. And the Lord will be named with an eternal sign, which will not be taken away.

< Ishaya 55 >