< Ishaya 55 >
1 “Ku zo, dukanku masu jin ƙishi, ku zo wurin ruwaye; ku kuma da ba ku da kuɗi, ku zo, ku saya ku kuma ci! Ku zo, ku saya ruwan inabi da madara ba tare da kuɗi ba ba za ku kuma biya kome ba.
“Biuru un duto ma riyo oloyo, biuru mondo umodh pi, adier biuru un ma uonge pesa, mondo ungʼiew kendo uchiem! Biuru ungʼiew divai gi chak nono maonge chudo.
2 Don me za ku kashe kuɗi a kan abin da ba abinci ba, ku kuma yi wahala a kan abin da ba za ku ƙoshi ba? Ku saurara, ku saurare ni, ku kuma ci abin da yake da kyau, ranku kuma zai ji daɗin abinci mafi kyau.
Angʼo momiyo utiyo gi pesa kungʼiewo gik ma ok chiemo kendo utiyo matek gi luchi ne gima ok yiengʼu. Winjuru, ee winjauru kendo ucham gima ber, mi unubed gi mwandu mar chuny.
3 Ku kasa kunne ku kuma zo gare ni; ku saurare ni, don ranku ya rayu. Zan yi madawwamin alkawari da ku, zan nuna muku ƙaunata marar ƙarewa da na yi wa Dawuda alkawari.
Chik iti kendo ibi ira, winj gima awacho mondo chunyi obed gi kwe. Abiro loso singruok mosiko kod herana mar adier mane asingone Daudi.
4 Duba, na mai da shi shaida ga mutane, shugaba da kuma jagorar mutane.
To ne, asemiyo obedo janeno e kind ogendini, kendo asekete obedo jatelo mar ogendini.
5 Tabbatacce za ku kira al’umman da ba ku sani ba, kuma al’umman da ba ku sani ba za su sheƙo a guje zuwa wurinku, saboda Ubangiji Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya darjanta ku.”
Chutho iniluong pinjeruodhi mane ok ingʼeyo mabi iri, kendo pinjeruodhi mane ok ongʼeyi malongʼo nobi iri, nikech Jehova Nyasaye ma Nyasachi, Jal Maler mar Israel osewiri kod duongʼne.”
6 Ku nemi Ubangiji tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.
Dwar Jehova Nyasaye ka pod thuolo nitie minyalo yudego; chutho luonge kapod en machiegni.
7 Bari mugu ya bar irin halinsa mugu kuma ya sāke irin tunaninsa. Bari yă juyo ga Ubangiji, zai kuwa ji tausayinsa, ya juyo ga Allahnmu kuma, gama shi mai gafartawa ne a sauƙaƙe.
Ngʼama timbene achach mondo owe yorene, kendo ngʼama parone opongʼ gi timbe richo mondo owe. Onego oduog ir Jehova Nyasaye, kendo enobed gi ngʼwono kuome mi enowene richone.
8 “Gama tunanina ba tunaninku ba ne, yadda kuke yin abubuwa ba yadda nake yin abubuwa ba ne,” in ji Ubangiji.
“Nimar parona ok e paroni bende yorena ok e yoreni,” Jehova Nyasaye owacho.
9 “Kamar yadda sammai suke can nesa da ƙasa, haka yadda nake yin abubuwa suke dabam da yadda kuke yin abubuwa tunanina kuma dabam da naku.
“Mana kaka polo bor gi piny e kaka bende yorena boyo maloyo mau, kendo e kaka parona ohewo parou.
10 Kamar yadda ruwan sama da dusar ƙanƙara suke saukowa daga sama, ba sa komowa ba tare da sun jiƙe duniya sun kuma sa su yi’ya’ya su kuma yi toho, don su ba da iri ga mai shuki da kuma abinci ga mai ci,
Mana kaka koth gi pe lwar koa e polo, kendo ok dog nono ka ok omiyo piny ngʼich, ma cham twi kendo nyag kothe ne jachwoyo, kendo cham ne jachiemo,
11 haka maganata da take fitowa daga bakina. Ba za tă koma gare ni wofi ba, amma za tă cika abin da nake so ta kuma cika abin da na aike ta tă yi.
e kaka wachna mawuok e dhoga, ok noduogna nono ka ok otiyo tije, to nyaka ochop dwarona, kendo otiek tijno mane omiyo aore.
12 Za ku fita da farin ciki a kuma bi da ku da salama; duwatsu da tuddai za su ɓarke da waƙa a gabanku, dukan itatuwan jeji kuma za su tafa hannuwansu.
Unuwuog kuno gi mor kendo notelnu gi kwe, gode madongo gi matindo nower matek e nyime kendo yiende duto manie bungu nopam gi ilo.
13 A maimakon sarƙaƙƙiya, itacen fir ne zai tsiro, a maimakon ƙayayyuwa kuma, itacen ci-zaƙi ne zai tsiro. Wannan zai zama matuni na abin da Ni Ubangiji na yi, madawwamiyar alama ce, wadda ba za a datse ba.”
Kuonde ma yande pedo ema nitie, nonyag olemo mabeyo mag yiend obudo, kendo kar kudho ema ochwoga mamit nodongie. Mano nomi Jehova Nyasaye huma maduongʼ, to gi ranyisi manyaka chiengʼ ma ok nomuki.”